Tarihin Fatima Zahra [a.s]



An ruwaito daga Jabir ATansari yana cewa Manzo ya ga Fatima da fatar rakumi tana nika tana kuma shayar da danta, sai idanuw ansa suka cika da hawaye. Sai ya ce: "Ya diyata ki yi hakuri da wahalhalun duniya don samun rabo mai yawa raii kiyama." Sai ta ce: "Ya Manzon Allah kullum godiya muke a kan niimomin da Allah ya yi mana masu yawa. Sai Allah ya saukar da ayar da taketewa: 'Da sannu Ubangijinka z.ai ta ba ka har sai kayarda."

An ruwaito daga Anas bin Malik yana cewa: Wata rana Bilal ya yi jinkirin kiran salla. sai Manzo ya tambaye shi abin da ya tsare shi. Sai ya ce: "Na zo uucewa sai na ga Fatima tana rtika ga yaranta na kuka Sai na cs mata da wanne zan taimaka miki? Sai na tsaya na taimaka mata da nikan'"

An ruwaito daga Suwaida Ibn Gafla yana cewa: Aliyu (AS) ya shigacikin wani kunci na rashi. sai Fatima (AS) taje gurin Manzo (SAW). sai ta kwankwasa masa kofa. Sai ya ce "Ina jin motsin abar kaunata a bakin kofa, tashi ki bude mata ya Ummi Aiman." Sai ta bude mata. sai ta shiga. Sai Manzo ya ce ''Lafiya na gan ki cikin wannan lokacin?" Sai ta ce: c'Ya Manzon Allah menene abincin Mala?iku a waajen Ubangijinsu?"" Sai ya ce "Tahamid." Sai t ace  "Mene ne abincinmu sai ' Sai ya ce "Na rantse da wanda raina. Yakw hannunsa yau kusan watanmu guda bam u hura wuta ba a gidanannan(don dafa abinci)ban a sanar da ke wasu kalmomi biyar ba, wadanda Malaika Jibril ya sanar da ni?" Sai ta ce "Wadanne kalmomi ne ya Rasulullah?" Sai ya ce: Ya Rabhal Awwalina wal akhirina, ya zalkuyywatil matin, ya rahimal masakin, ya arhamur rahmin. Lokacin da Aliyu (AS) ya ga Nana ta dawo sai ya ce mata me ta samo? Sai ta ce "Na je don warware matsalar duniya na dawo da rabon lahira." Sai ya ce "'madalla da rabon lahira."

An ruwaito daga Imran Bin Husain yana cewa: Wata rana muna zaune gurin Manzo sai Fatima ta taho, sai ta zauna a gabansa. Sai ya dubi fiiskarta sai ya ga alamar rama sosai. Sai ya ce mata ta matso. Daga nan sai ya sa hannunsa a kirjinta. Sannan sai ya yi mata addu'a yana cewa: "'Ya Ubangijin da yake kosar da mai jin yunwa, wanda yake daukaka na kasa, ka raba Fatima binti Muhammad da jin yuriwa." Daga nan sai alamar koshi ya bayyana a fuskarta. Tun daga wannan ranar Fatima (AS) ba ta kara jin yunwa ba har ta koma ga Ubangijinta Madaukaki.

Wata ranaManzo ya zo gai da Fatima (AS) bata da lafiya, sai ya ce mata yaya jiki° Sai ta ce "'Ni matukar yunwa nake ji. kuma yana kara min zafin ciwo. Ba ni da wani abmci da zan ci yanzu." Sai Manzo ya ce 'In wannan ya bakanta miki. kasantuwarki Shugabar matan duniya baki daya. ai sai shi kuma ya faranta miki.

INFAKIN NANA FATIMA (AS)

An ruwaito daga Ibn Abbas yana cewa; Hasan da Husain sun yi rashm lafiya sai Manzo ya zo ya gai da su. Sai ya ce wa Aliyu "Da za ku yi alawashi in Allah ya ba su lafiya za ku yi wani abu na ibada " Sai suka yi alwashin yin azumi dukkansu (Aliyu. Fatima. Hasan. Husain. Fizza) a kan in sun sami lafiya za su yi azumi uku. sai suka sami lafiya Fatima tana da sai uku na shair. sai ta nika sai daya ta yi waina guda biyar yadda kcma zai samu guda-guda. Lokacin da shan ruwa ya yi sun dauko za su ci sai ga mai bara ya zo yana cewa :Assalamu alaikum Ahlul bait Muhammad" Miskini ne daga cikin miskinan musulmi yake bara. ku ciyar da'shi. Allah ya ciyar da ku abincin Aljanna." Sai suka ba shi abincin duk ba su ci komai  ba , suka  kwana haka

Washegari kuma suka ta shi azumi  na biyu. Shi ma kamar haka sun zo za su yi buda baki, sai wani yatimi  (maraya) ya zo ya yi musu bara kamar irin na jiya. sai suka ba shjabiricin suka kwana ba su ci komai ba.

A kwana na uku, shi ma sun tashi  ba tare da su ci komai ba .lokacin shan ruwa ya yi ,sun zo za su yi buda baki, sai wani Asi

(Bursunan yaki) ya zo kamar jiya da shekaran jiya ya yi bara. Sai suka ba shi abincin baki daya ba tare da sun ci komai ba tsawon kwana uku.

Washegari sai Aliyu ya kama hannun Hasan da Husain ya nufi gurin Manzo. Da Manzo ya hango su sun yi rama sosai, sai ya mike yana cewa "Wane irin bakin ciki zan gani yauF' Sai ya ce su juya gaba daya zuwa guda. Ko da sukaje gida sai ya tarar da Fatima idanunta sun fada, cikinta ya shafe da bayanta saboda yunwa. Sai ya ce "Yau wane irin bakin ciki nake gani." Daga nan sai Malaika Jibrilu ya sauko da yyahayi-ya ce: "Madalla da irin wannan gida naka." Sai ya karanta masa: "Lallai masu nagarta..." har zuwa karshen ayar.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 next