Tarihin Fatima Zahra [a.s]



GALIB IBN FIHIR: Sunan mahaifiyarsa Laila. An haife shi ne a shekara ta 23^~bayan zuwan Annabi Isa (as). Bayan rasuwar mahaifinsa shi ne ya zama shugaban mutaiiensa. bayan wannan hasken ya koma ya zuwa gare shi.

LU'Ay YI IBN GALIB: Sunan mahifiyarsa Salnia An haite shi ne a shekara ta 266 bayan zuwan Annabi Isa (as). Bayan wafatin mahaifinsa sai wannan hasken ya koma ya zuwa gare shi

KA'AB IBN LU'AYYI: Sunan mahaifiyarsa Mariya. An haife shi ne a shekara ta 299 bayan zuwan Annabi Isa (as). Bayan rasuwar mahaifinsa sai wannan hasken ya koma ya zuwa gare shi Ya kasance abin girmamawa a cikin Larabawa sosai Gidansa ya zama mafakar miskinai dafakirai. Lokacin da ya rasu Larabawa sun yi juyayin mutuwarsa kwarai. Daga wannan shekarar suka faro kidayar shekam har zuwa lokacin da Abrahata ya zo zai rusa Ka'aba. Allah ya halaka shi Sun yi lissafi da shekarar da ya rasu a kan ya rasu ne a shekara ta 5644 bayan saukowar Annabi Adam (as) daga Aljanna.

MURRA IBN KA'AB: Sunan mahaifiyarsa Mahashiyyatu. An haife shi ne a shekara ta 332 bayan zuwan Annabi Isa (as). Bayan rasuwar mahaifinsa. sai wannan hasken ya koma ya zuwa gare shi.

KILAB IBN MURRA: Sunan mahaifiyarsa Hindu. An haife shi ne a Shekara ta 368 bayan zuwan Annabi Isali (as). Bayan rasuwar mahaifmsa, sai wannan hasken ya koma ya zuwa gare shi.

KUSAYYI IBN KILAB: Sunan mahaifiyarsa Fatima. An haife shi ne a shekarata 398 bayan zuwan Annabi Isa (as). Ya zama shugaban jama'arsa bayan rasuwar mahaifinsa.

ABDULMANAF IBN KUSAYYI: Sunan mahaifiyarsa Hubbi. An haife shi ne a shekara ta 430 bayan zuwan Annabi Isa (as). Ana masa lakabi da farin wata BADAHA’U (cikin garin Makka) saboda kyawun fuskarsa. Bayan rasuwar mahaifinsa, sai wannan hasken ya koma ya zuwa gare shi.

HASHIMIBN ABDUL MANAF: Sunan mahaifiyarsa Atika binti Murra. An haife shi ne a shekara ta 464 bayan zuwan Annabi Isa (as). Bayan rasuwar mahaifinsa, shi ne ya zama shugaban mutanensa, bayan wannan hasken ya koma zuwa gare shi. Shi ma mun riga mun yi bayaninsa a baya.

ABDUL MUDALLIBIBN HASHIM: Sunan mahaifiyarsa Salma binti Amru. An haife shi ne a shekara ta 497 bayan zuwan Annabi Isa (as). Wata rana Hashim ya tafi Ka'aba da daddare. ya kaiikan da kansa. ya roki Allah ya ba shi da wanda zai gajc shi. sai ya yi mafarki an ce masa ya jc ya aun Salma binti Amm a can Madina.

Lokacin da ya je sai ya sauka a gidan Mahaifinta. ya nemi izni aka ba shi. daga karshe aka aurar niasa da ita a kan sharadm in za ta haihu zai komo da ita Madina ta haihu a gida. Lokacin da ta samu ciki sai ya koma da ita gidansu a kan hanyarsa ta zuw a Sham. Wanda a hanyarsa ta dawowa ya rasu



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 next