Ahlul Baiti



A mulkin Al-Hadi, sarkin Abbasiyawa, ne bala'i ya tsananta kan Imam (a.s.) da kuma Alu Ali (a.s.). Ya ci gaba da korarsu da kashe su da neman batar da su gaba daya musamman ma bayan yunkurin Husain bn Ali wanda aka fi sani da waki'ar Fakh. Imam Kazim (a.s.) ya gamu da tsanantarwa da matsarwa har sai da ta kai Al-Hadi din ya hukumta Imam (a.s.) da hukumcin kisa ya kuma tasanma aiwatar da hakan. Malaman tarihi sun ruwaito cewa alkali Abu Yusuf almajirin Imam Abu Hanifa shi ne ya shiga tsakanin Al-Hadi da wannan kuduri da ya dauka na kashe Imam Kazim (a.s.), don Al-Hadin ya zaku kan kashe Imam (a.s.) har cewa ya yi: "Allah ya kashe ni idan na yi wa Musa ibn Ja'afar afuwa".

Daga nan sai Al-Hadi ya sanya Imam Kazim (a.s.) a kurkuku da hana shi damar gudanar da aikinsa na ilmantarwa da jagoranci a bayyane. Amma mutuwa ba ta bar shi ya aikata mummunan nufinsa, don kuwa ta kawo karshen wannan azzalumi jabberi.

Daga nan sai lokacin Haruna Rashid wanda aka sami jayayya mai tsananin gaske tsakaninsa da Imam Kazim (a.s.). Haruna Rashid ya yi kiran Imam da ya taho daga birnin Madina zuwa Iraki, inda ya ci gaba da tozarta shi da sanya shi a kurkuku da azabtarwa nau'i daban-daban, wadanda suka hada da daure shi da karfe yana daukansa daga wannan kurkukun zuwa wancan. Imam (a.s.) ya zauna a kurkuku tsawon shekaru, daga karshe Haruna Rashid ya ci da shi guba ta hannun shugaban dogarawan-sa mai suna Al-Sandi bn Shahik. Imam (a.s.) ya yi shaha-da ne a ranar 25 ga watan Rajab a shekara ta 183 bayan hijira.

Daga nan sai zamanin Imam Ridha, Aliyu bn Musa bn Ja'afar (a.s.), wanda shugabancinsa na siyasa ya wajabtawa Abbasiyawa la'akari da shi a sakamakon karfin alkadarin Imam (a.s.) da kaunar al'umma gare shi ga kuma tsanantar bijirewa ga Abbasiyawa. Wannan yanayi ya tilastawa halifan Abbasiyawa Ma'amun sanya Imam (a.s.) a matsayin magajinsa. Imam Ridha (a.s.) ya karbi wannan matsayi ba don sonsa ba, kana kuma da sharadin cewa shi ba zai shiga harkokin shugabanci ba, sannan idan Ma'amun ya mutu, halifanci zai koma hannunsa. To amma Imam Ridha (a.s.) ya yi shahada yayin da Ma'amun ya ba shi guba a shekara ta dari biyu da uku bayan hijira.

To bayan shahadar Imam Ridha (a.s.), wanda ya karbi jagoranci al'umma da lamarin Imamanci shi ne dansa Imam Muhammad Jawad (a.s.) wanda ya yi zamani da Ma'amun na dan lokaci. Ma'amun ya yi mu'amala da shi da girmamawa a munafunce, ya aurar masa da 'yarsa Ummul Fadhl domin ya sami soyayyar al'umma, yayi hakan ne kuwa domin ya juya hankulan mutane ya karkata ra'ayin masu gaba da shi, wadanda suke ganin Imam (a.s.) a matsayin jagora. Sai dai fa Ma'amun bai tsinana komai ba domin Imam Jawad (a.s.) ya bar Bagadaza ya koma birnin Kakansa Manzon Allah (s.a.w.a.) saboda ci gaba da aikinsa na ilmantarwa da jagorancin al'umma a can.

To bayan da Ma'amun ya mutu sai dansa Al-Mutasim ya hau karagar mulkin Abbasiyawa, sai dai kuma shi Al-Mutasim bai jima a kan mulkin ba, to amma dai shi ma ya kasance yana jin tsoron Imam Jawad (a.s.) da kuma hadarin zamansa a Madina. To shi ma Al-Mutasim bai yi wata-wata ba sai ya kama tafarkin iyayensa yayin da ya dauko Imam daga Madina ya kawo shi helkwatarsa domin ya sanya ido a kansa. Marubuta tarihi sun ce Imam Jawad (a.s.) ya yi shahada ne a hannun Mutasim ta hanyar guban da ya sa masa cikin abinci a shekarar da ya kawo shi Bagadaza a lokacin kuwa hijira tana da shekara dari biyu da ashirin da biyar.

To bayan shahadar Imam Jawad (a.s.) dansa Imam Ali Hadi shi ne ya gaji jagorancin al'umma da Imamanci daga mahaifin nasa. A zamanin Mutawakkil Abbasi ne Imam Hadi (a.s.) ya fuskanci keta da cutarwar Abbasiya-wa. Mutawakkil da ma sananne ne da son wasa da kuma gaba da Alayen Manzon Allah (s.a.w.a.) da kashe su da korar su da yanke abincinsu da hana mutane taimakonsu. Imam Hadi (a.s.) ya kasance yana tsorata halifa Mutawakkil saboda haka sai ya dauko shi daga Madina ya kai shi garin Samarra ya sa ido sosai a kansa, ya kuma tilasta masa zama a can. To lokacin da al'amurra suka yi zafi wa Mutawakkil, sai ya fara barazanar kisa ga Imam Hadi (a.s.) baya ga daure shi da ya sha yi. A wasu lokuta ya kan sa a binciki gidan Imam Hadi (a.s.) da kai hari wa gidan, bugu da kari kan tsananta sanya ido a kansa saboda tsoron irin tasirin da Imam (a.s.) yake da shi a idon al'umma.

Marubuta tarihi sun ambaci dalilan da suka sa Mutawakkil ya ta da Imam Hadi (a.s.) daga Madina. Sibt Al-Jawziyya ya ce:

"Malaman tarihi sun ce: Ya fito da shi daga Madinar Manzon Allah (s.a.w.a.) zuwa Bagadaza ne don yana tsananin kin Aliyu da zuriyarsa sai kuma ya sami labarin irin matsayin Aliyu Hadi a Madina da karkatar mutane zuwa gare shi. Wannan ya sa shi tsoronsa([245])".

Bayan shahadar Imam Hadi (a.s.) garin Samarra a shekara ta 254 bayan hijira, sai dansa Imam Abu Muhammad Hasan Askari (a.s.) ya kasance Imami mai kula da harkar al'umma da kuma shiryar da su. To shi ma dai matsayinsa kan Abbasiyawa tamkar na iyayensa ne, wajen fito-na-fito a fagen siyasa. To shi ma dai mahu-kumtan ba su bar shi don kuwa sun cutar da shi kamar yadda suka cutar da mahaifansa. Al-Muhtadi bn Al-Wasik sarkin Abbasiyawa ya sanya shi a kurkuku a garin Samarra, inda ya mika shi ga hannun gandurobobin kurkukun wadanda suka shahara da mugun hali da zalunci don azabtar da shi, amma Imam (a.s.) ya yi tasiri kansu har suka shiryu suka zamo mutanen kwarai.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 next