Ahlul Baiti



Saboda haka a tafarkin malaman fikihu da malaman mazhabar Ahlulbaiti (a.s) Imamiyya ba a samun:

1.  Rikon wani littafi na hadisi a matsayin sahihi daga dayansa ko kuma kore shi gaba dayansa.

2.  Su suna karbar ruwayar maruwaici ne bisa sharadin gaskiyarsa da amincinsa ba tare da lura da mazhabarsa ko bangaren da ya fito ba.

Wanda duk yake bitar littattafan Usulu da fikihu da Ilmul Rijal , zai samu wannan hakikar a bayyane.

Da haka ne wannan hanyar bin diddigi ta ilmi ta kiyaye asalin shari'a da tsarkin ta, da kuma hadin kan musulmi da nisantar nuna bangaranci, jahilci da ganin girman wani tun da ba a ba da dama wa wadannan abubuwa a tafarkin bincike, don kuwa a yayin bincike kowa daya ne.

Kuma da wannan tafarkin bincike da ilmin bin diddigi, wanda ya kafu a bisa asasin neman gaskiya da bincike a aikace, da rashin mika wuya da yarda da ingancin kowace ruwaya ba tare da lura da kowane ne maruwaicin ta ba, ko littafin da aka ruwaito ta ba, ne ake gudanar da binciken hadisi.<

Imaman Ahlulbaiti (a.s) Maruwaita Manzon Allah (s.a.w.a)

Imaman Ahlulbaiti (a.s) ba su kasance masu Ijtihadi ko fitar da hukumci ba, sai dai sun kasance masu ruwayar Sunna ne, don haka, duk abin da ya fito daga gare su Sunna ce. Su kan ruwaito Sunnar ce da daga mahaifinsa, daga kakansa….daga Manzon Allah (s.a.w.a.). A saboda haka ne Imam Sadik (a.s.) ya ke cewa: "Hadisina hadisin babana ne, hadisin babana hadisin kakana ne, hadisin kakana hadisin babansa ne, hadisin babansa kuwa hadisin Aliyu bn Abi Talib ne, hadisin Aliyu kuwa hadisin Manzon Allah (s.a.w.a.) ne, hadisin Manzon Allah (s.a.w.a.) kuwa fadar Allah ce Mai girma da Daukaka([131])".

Daga Kutaiba, ya ce: "Wani mutum ya tambayi Abu Abdullah al-Sadik (a.s.) wata mas'ala, sai ya ba shi amsarta, sai mutumin ya ce: mene ne ra'ayinka in ya kasance kaza da kaza, mene ne hukumcinsa? Sai Imam ya ce masa: "Saurara! Abin da na baka jawabinsa, to daga Manzon Allah (s.a.w.a.) ya ke, mu ba mu daga cikin wadanda a ke ce da su mene ne ra'ayinka a kowane abu([132])".

A saboda haka ne Shaikh al-Baha'i yake cewa:



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 next