Ahlul Baiti



Wadannan ra'ayoyi kuwa su ne:

1.  Jabru (Tilastawa).

2.  Tafwidhu (Sakarwa).

3.  Babu Jabru ballantana Tafwidhu.

Hakika wadansu kungiyoyi da mazhabobi sun yi mummunan fahimta wa zahirin wadansu ayoyin Alkur'ani, kamar fadinSa (S.W.T.) cewa:

".
Zahirinsu ya sanya irin wannan kungiya suka yarda da Jabru. Abin da wannan ra'ayi yake nufi shi ne dan'Adam ba ya mallakar nufi kuma ba shi da zabi, shi ba kome ba ne face bigire da gurin saukar kaddararrun abubuwa daga Allah (S.W.T.). A bisa wannan ra'ayi, mutum abin tilastawa ne, ba shi da wani zabi cikin al'amurransa. Masu irin wannan ra'ayi ana kiransu da sunan Mujabbira.

Ra'ayi na biyu kuwa shi ne mai cewa an sakar wa dan'Adam ikon zabi wajen ayyukansa, da kuma nufinsa babu nufin Allah a cikin ayyukansa. Kai suna ganin ma cewa Allah ba Ya iya hana mutum yin abin da ya yi nufin yi ko sabo ne kamar kisan kai, zalunci, shan giya, ko kuwa ayyukan biyayya ne kamar su adalci, kyautatawa, salla da dai sauransu. To da wannan, dan'Adam yana da 'yanci ga barin Allah (S.W.T.), wannan kuwa shi ne ra'ayin Mu'utalizawa.

To Imaman Ahlulbaiti (a.s) sun yi raddi wa wadannan ra'ayoyi guda biyu, sun nuna bacinsu gaba daya. Kowanne daga ra'ayoyin nan biyu sun saba da abin da Alkur'ani ya zo da shi, akidar tauhidi kuwa ta kafu kan tushensa ne. su Imamai (a.s.) sun fayyace mana cewa akwai bayyananniyar alaka tsakanin irin yadda ake fahimtar halayyar mutum da imani da adalcin Allah. Suka ce lallai abin da ra'ayin cewa mutum ba ya mallakar wani nufi ko zabi sai dai shi abin tilastawa ne kurum, yana janyo tuhumtar Mahalicci Mai girma da Daukaka da zalunci da kore adalci daga gare Shi, lallai kuwa Ya girmama daga hakan. Saboda ma'anar wannan shi ne Allah Ya tilastawa mutum aikata sharri sannan kuma Ya yi masa ukuba dominsa, haka nan Ya tilasta masa aikata alheri sannan kuma Ya hana shi ladansa. Domin haka ne Imamai (a.s.) suka kakkabe wannan
mumunan fassara wanda da yawan musulmi suka fada ciki a dalilin gurguwar fahimtar da suka yi wa zahirin wadansu ayoyi kamar cewa:

"Yana batar da wanda Ya so, Yana kuma shiryar da wanda Ya so".

Imaman Ahlulbaiti (a.s) sun yi wa matsalolin shiryarwa da batarwa tafsiri bayyananne mai dacewa da adalcin Allah (S.W.T.). Bayanin wannan yana tafe.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 next