Ahlul Baiti



 

Yazid dan Mu'awiyya, shi ma ya dauki mataki irin na ubansa akan Imam Husain (a.s.), ya kashe shi tare da mutanen gidansa, ya ribaci zuriyar Manzon Allah (s.a.w.a.) yayin da Imam Husaini (a.s.) ya jagoranci yunkurin bijirewa hukumar Banu Umayya ta zalunci da aka tilasta ta a kan al'umman musulmi.

Bayan Imam Husaini (a.s.) ya yi shahada, musulmi sun karkata hankalinsu ga Imam Ali bn Husain, Zainul Abidin (a.s.), suna ganinsa a matsayin wata alama kana kuma makoma gare su, don haka ne masu yunkuri

gwagwarmaya suke neman izininsa. Don haka ne ma a zamaninsa an sami masu jihadi domin kare Ahlulbaiti (a.s) da yawa, kamar yunkurin Madina da Makka da na Mukhtar Al-Thakafi da na Tawwabun, dukkansu suna yaki domin daukar fansa kan wadanda suka kashe Imam Husaini (a.s.). A wancan lokacin mutane suna ganin Imam Zainul Abidin a matsayin kololuwar bijirewa azzalumai duk da cewa bai motsa ba. Matsayin da ya dauka kan Yazid bn Mu'awiyya da Marwan bn Hakam da Abdul Malik bn Marwan da sauran azzaluman mahukunta, matsayi ne na mai bijirewa a asirce da taimakon masu yunkuri ba tare da shelar hakan ba. har ma Imam (a.s.) ya roki rahamar Allah ga Mukhtar, wanda ya dauki fansa kan wadanda suka kashe Imam Husaini (a.s.) ya kuma yaba da jihadin Mukhtar. Sannan kuma Imam (a.s.) ya yi amfani da makamin addu'a([239])(*) mai bayyana irin ra'ayinsa na siyasa da akida, mai sabawa da ra'ayin su Yazid.

Imam Bakir (a.s.) dan Imam Zainul Abidin (a.s.) shi ma ya nuna matsayin da yake kai na bijirewar siyasa daga Banu Umayya. Imam ya sha wahala kwarai a hannunsu, musamman ma Hisham bn Abdul Malik mai bayyana kiyayya da gaba ga Alawiyyawa. A zamaninsa ne Zaid bn Ali dan uwan Imam Bakir (a.s.) ya fito jihadi.

Shi dai wannan halifa na Banu Umayya ya tabbatar cewa tushen wannan yunkuri na Zaid daga Imam Bakir da dansa Ja'afar Sadik (a.s.) yake. Don haka sai ya kira su daga Madina zuwa ga helkwatarsa da ke Sham, yayin da Imam Bakir (a.s.) ya shiga fadar Hisham sai ya yi sallama yana nuni zuwa ga mahalarta majalisar, amma bai yi gaisuwar sarauta ga halifan ba. Sai Imam ya zauna ba tare da da wani izinin sarki ba, hakan ya kara wa Hisham kiyayyarsa ga Imam har ma ya kama sukansa da cewa:

"Ya Muhammad bn Ali, ko yaushe sai an sami wani mutum daga cikinku yana raba kan musulmi, da kiran jama'a don su bi shi, domin wauta da karancin ilmi".

Sai Hisham ya ci gaba da suka, jama'ar da ke fada su ma suka fara sukar Imam din bayan Hisham ya yi shiru. Da ganin wannan ka san cewa an umurce su da hakan ne kafin ma Imam din ya shigo tare da dansa, Imam Sadik (a.s.). Ganin haka ke da wuya, sai Imam Bakir (a.s.) ya mike tsakiyar majalisar yana mai raddi ga sarki da cewa:

"Ya ku mutane! Ina kuke zuwa ne? Ina aka nufa da ku ne? Da mu Allah Ya shiryar da farkonku, da mu kuma Zai cika (shiryar) da na karshenku. Idan kuna da mulki abin gaggautarwa, to mu muna da mulki da aka jikirta, kuma babu wani mulki bayan namu, domin mu ne masu mulkin karshe".

Allah Madaukakin Sarki Yana cewa:



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 next