Ahlul Baiti



3.  Al-Tahzib na Shaikh Dusi.

4.  Man la Yahdhuruhul Fakih na Shaikh Saduk.

5.  Wasa'il al-Shi'a na Hur al-Amuli.

6.  Biharul Anwar na Allama Majlisi.

Da dai sauran littattafan hadisi.

Babu shakka malaman Imamiyya wadanda kuma suke lizimtar tafarkin Ahlulbaiti (a.s) a fikihu da shar'antawa da ilmomin Musulunci sun sanya hadisan da suka zo cikin wadannan littattafa a bisa ma'aunin bincike wanda ya kubuta daga son rai, inda bayan binciken suka zubar da adadi mai yawa na hadisan saboda rashin ingancinsu.

Kamar yadda wadannan malumma suka binciki wadannan littattafa na hadisi, haka kuma suka gudanar da bincike kan wasu littattafan kuma, kamar su Sahih Bukhari, Sahih Muslim, Sunan Abi Dawud, Kanzul Ummal da dai makamantansu daga cikin littattafan hadisai da ruwayoyi, suka kuma auna su da wannan ma'auni na ilmi, kamar dai yadda suka gudanar akan wadancan, suka dauki na dauka da kuma zubar da ba zubarwa.

Su wadannan malamai kuwa, su kan yi wannan bincike nasu ne a bisa wadannan asasai:

Sai ya ce: "Abin da ake nufi da 'Khatam' shi ne 'al-Dab'u' watau rufi a kan zukatan kafirai domin yi musu ukuba kan kafircinsu, kamar yadda Allah (S.W.T.) ya ce:

"A'a Allah ne Ya rufe a kansu (zukatansu) saboda kafircinsu, saboda haka ba za su yi imani ba face kadan([186])". (Surar Nisa', 4: 155)



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 next