Akidojin Imamiyya



[19] - Mujabbira, da Ash’ariyya suna da wannan ra’ayi da aka san shi da jabar na musun wasida da tsakanin da Allah ya halitta ya kuma sanya shi tsakaninsa da bayinsa da falalarsa, kamar ‘ya’yan mangwaro da suke zuwa daga itace, wato sai suka ce kai tsaye Allah ne ya halitta su ba tare da wata rawa da shuka a matsayinta na wasida ta taka ba. Wannan shi ne kwatankwacin ayyukan bayinsa a wajansu, don haka kai tsaye ayyukansu ayyukansa ne.

[20] - Sabanin Mujabbira da Ash’ariyya, Mu’utazilawa sun tafi akan Tafwidi da ma’anarsa take nufin cewa babu hannun Allah a cikin ayyukan bayi ko kadan, wannan ra’ayi da shi da na farkon duka a gun mazhabar imamiyya kuskure ne.

[21] - “Da rai da abin da Ya daidaita ta kuma ya cusa mata fajircinta da kuma takawarta”. Surar Shamsi: 7-8.

[22] - Adifa al’amura ne kamar ki, so, fushi, yarda, da sauran halayen rai da zuciya.

[23] - “Manzanni masu bushara kuma masu gargadi domin kada mutane su zama suna da wata hujja a kan Allah bayan Manzanni kuma Allah mabuwayi ne Mai hikima”. Surar Nisa’i: 165.

[24] - “Kuma sai muka yi wahayi ga Musa kan cewa jefa sandarka sai ga shi tana hadiddiye abubuwan da suke kirkira. Kuma gaskiya ta tabbata abin da suke aikatawa kuma ya baci, Sai aka rinjaye su a nan sa’annan suka juya suna kaskantattu, Kuma aka kifar da masu sihirin suna masu sujada”. Surar A’araf; 117-120.

[25] - “Kuma Manzo zuwa ga Bani Isra’ila cewa lalle ni na zo muku da aya daga Ubangijinku ni ina halitta muku daga laka abin da yake kamar surar tsuntsu kuma in hura a cikinsa sai ya zamanto tsuntsu da izinin Allah kuma ina warkar da makaho da mai albaras kuma ina raya matattu da izinin Allah kuma ina ba ku labarin abin da kuke ci da wanda kuke taskacewa a gidajenku lalle a cikin wannan akwai aya gare ku idan kun kasance muminai”. Surar AI- Imran: 49.

[26] - Duba fadin Allah madaukakin sarik:

 â€œKuma idan da mutane da aljannu zasu taru a kan su zo da kwatankwacin wannan Alkur’anin to da ba zasu zo da makamancinsa ba koda kuwa sashensu na taimakon sashe”. Surar Isra’i: 88.

“Ko suna cewa shi ne ya kage shi ne ka ce to ku zo da surori goma makamantansa kagaggu kuma ku kira duk wanda za ku iya wanda ba Allah ba in kun kasance masu gaskiya”. Surar Hud: 13



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 next