Akidojin Imamiyya



Sai ya ce da ni: Ya Safwan duk wani abu daga gareka kyakkyawa ne mai kyau in banda abu daya.

Na ce: A sanya ni fansa gare ka! Wane abu ne?

Ya ce: Ba da hayar rakumanka ga wannan mutumin wato Harunar Rashid.

Na ce: Wallahi ni ban ba shi haya ba ina mai ashararanci, ko dagawa, ko don farauta, ko wasa ba, sai dai na ba shi haya ne don wannan tafarkin wato hanyar Makka kuma ba na aikin da kaina sai dai ina tura shi da bayina.

Ya ce: Ya Safwan kudin hayarka yana zama bashi a kansu?

Na ce: Na’am, a sanya ni fansa gare ka.

Ya ce: Shin kana so su wanzu har su biya ka kudin hayarka?

Na ce: Na’am.

Ya ce: To duk wanda ya so wanzuwarsu yana cikinsu, duk wanda ya kasance daga cikinsu shi mai shiga wuta ne.

Safwan ya ce: Sai na tafi na sayar da rakumana baki daya.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 next