Akidojin Imamiyya



Sai ya ce: Ya Mu’ula ni ina mai tausasawa gareka, ina tsoron ka tozarta ba za ka kiyaye ba, ko kuma ka sani ba za ka aikata ba.

Na ce: Babu karfi sai da Allah.

Yayin nan sai Imam (A.S) ya ambaci hakkoki bakwai bayan ya fada game da na farkonsu: “Mafi saukin hakki daga cikinsu shi ne ka so wa dan’uwanka kamar yadda kake so wa kanka, ka kuma ki masa abin da kake ki wa kanka”.

SubhanalLahi! Wannan shi ne hakki mai kankanta to yaya wannan hakkin mafi kankanta yake a gare mu yau mu musulmi? Kaicon fuskon da suke da’awar musulunci amma ba sa aiki da mafi kaskantar abin da ya wajaba na daga hakkoki. Abu mafi ban mamaki kuma shi ne a dangata wannan rashin ci gaban da ya samu musulmi ga Musulunci, alhalin laifi ba na kowa ba ne sai na wadanda suke kiran kansu musulmi amma ba sa yin aiki da mafi karancin abin da ya wajabta musu da su yi aiki da shi na koyarwar addininsu.

Domin tarihi kawai kuma don mu san kawukanmu da takaitawarta zamu ambaci wadannan hakkoki bakwai wadanda Imam (A.S) ya bayyana su:

l- Ka so wa dan’uwanka musulmi abin da kake so wa kanka, kuma ka ki masa abin da kake ki wa kanka.

2- Ka nisanci fushinsa ka bi yardarsa ka kuma bi umarninsa.

3- Ka taimake shi da kanka, da dukiyarka, da harshenka, da hannunka, da kafarka.

4- Ka zamanto idonsa, dan jagoransa, kuma madubinsa.

5- Kada ka koshi shi kuma yana cikin yunwace, kada ka kashe kishirwarka shi kuma yana jin kishirwa, kada ka zama a suturce shi yana tsirara.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 next