JOGARANCIN IMAM SADIK (A.S).



Shi halifa a musulunci yanan dauke da mas’u’liyyar siyasa da ta addini gaba daya. Wannan tabbataccen al’amari ya sa halifofin da suka zo bayan na farko, wadanda rabonsu a cikin ilmomi addini ya yi karanci ainun, ko kuwa basu da wani rabo sam, ya sanya su rufe wannan nakasu ta hanyar malaman addini  masu aikata musu abin da suke so. Sai suka baiwa fukaha’u da malaman tafsiri da na hadisi aiki a fada saboda tsarinsu na shugabanci ya tara sassan nan biyu: na addini da na siyasa.

Wata fa’idar samuwar masu wa’azin sarki a tsarin shugabanci, ita ce: azzalumin shugaba mai kama karya, a duk lokacin da ya so, yana iya canja wa hukunce-hukuncen addini fuska ko kuma ya musanya su dai-dai da bukatunsa. Wadancan ma’aikata, malaman fada, su suke aiwatar da wannan domin dadada wa masu azurta su. Suna yin haka ne karkashin rigar istinbadi da ijtihadi mai rudin jama’a.

Mawallafa da marubuta tarihi daga magabata sun ambato mana misalan da kare ba zai ci ba kan kirkirar hadisai da tafsiri da ra’ayi inda ake ganin hannun ikon siyasa a sarari. Za mu yi nuni da wani abu akai a nan gaba. Wannan al’amari wanda da farko(har zuwa karshen karnin farko bayan hijira) ya dauki salon kirkirar riwaya ko hadisi, sannu a hankali ya dauki matsayin fatawa. Daboda haka ne a karshen zamanin Banu Umayya da farkon na Banu Abbas muke ganin bayyanar fukaha’u masu yawa suna amfani da hanyoyin ka’idojin istinbadi masu rauni domin su kafa dokoki dai-dai da zabinsu wanda a kashin gaskiya zabin tsarin da yake shugabanci ne. A fagen tafsirin Alkur’an ma, kwatankwacin wannan aiki aka zartar. Tafsiri da ra’ayi, galibi, ya sa gaba wajen bayar da fahimce-fahimce wa musulunci, wadanda basu dogara da komai ba face zabin mai fassara da son ransa, wanda ba komai ba ne illa son ran tsarin da yake  shugabanci.

Wannan shi ne musabbabin rabuwar ilmomin musulunci: na fikihu da hadisi da tafsiri, tun zamunan na farko, zuwa ra’ayoyi biyu.

Ra’ayin Farko:- Ra’ayin da ke da alaka da tsarin azzulumar hukuma mai kwace. Yana bambata da dayan wajen sadaukar da gaskiya domin tabbatar da ‘maslaha’ wacce bisa hakika maslahar tsarin da ke shugabanci ne. Daga sifofin wannan ra’ayin har wala yau akwai  baudar da hukunce-hukuncen Allah domin, ladan  ‘yan dirhamomi.

Ra’ayin na Biyu:- Ra’ayi dan asali amintacce wanda ba ya ganin akwai wata  maslaha mai daraja da daukaka da ta wuce bayyana ingantattun hukunce-hukuncen Ubangiji. Wannan ra’ayi ya kasance, ko an ki ko an so, yana cin karo da tsarin da yake shugabanci da kuma masu wa’azin fada, a duk wani taku da ya yi. Saboda haka tun farkon al’amari ya dauki mafuskanta irin ta talakawa tare da taka tsan- tsan  da kiyayewa.

Fahimtar wannan zai sa mu gane da kyau cewa sabawan Fikihun Ja’afar da fukaha’un sarauta a zamanin Imam Sadik ba wai sabawa ce ta tunani da akida kadai ba, a’a ta hada har da abin da ya kunsa na hari irin wanda abokin hamayya yake yi.

Mafi muhimmanci daga kusurwowin wannan abin da ya kunsa shi ne tabbatar da cewa tsarin da ke shugabanci fanko ne kawai wanda ya rasa dukkan ma’anonin addini, ga kuma gajiyawarsa  wajen gudanar da al’amuran tunani ga al’umma. Ko kuma mu ce rashin cancantarsa hawa mukamin “halifanci”. Wata kusurwa ita ce ayyana wuraren da aka baude cikin fikihun sarauta, wadannan baude-baude da aka gina kan tunanin “maslaha”  wajen bayanin hukunce-hukuncen fikihu da sassautarwar malaman fikihu ga tsarin da ke shugabanci. Imam Sadik (a.s), da ayyukansa na karantarwa da kuma sabar nauyin bayyana hukunce-hukuncen fikihu da ilmomin musulunci  da tafsirin Alkur’ani ta hanyar da ta saba da ta masu wa’azin fada, hakika, a aikace, ya dauki matsayin hamayya da tsarin da ke mulki. Da wannan aikin, Imam ya iya watsi da duk tsarin sarauta a addini da fikihu wanda wani bangare ne na hukumar halifofi, ya kuma tube wa tsarin da ke mulki duk wata rigar addini.

Ba mu da wani tabbataceen isnadi mai bayyana lurar tsarin Umayyawa da wannan janibin hamayya, wanda Imam Sadik (a.s) ya aiwatar a fagen ilmi da fikihu. Sai dai abin da aka fi tsammani shi ne tsarin Abbasiyawa mai mulki-----musamman lokacin Mansur wanda yake mai wayo ne da gogewa da fahimtar halayyar duniya, abubuwan da ya koya a lokacin dambarwar siyasa mai tsawo tsakaninsa da mulkin Umayyawa kafin shi kansa ya sami mulkin--wannan tsarin nasu yana riskar mas’alolin masu wuyar fahimta da ke tattare da ayyukan gidan Ali. Kuma tsarin Abbasiyawa  mai mulki yana fahimtar muhimmiyar rawar da wancan aikin ilmi zai iya takawa  ta bayan fage.

Barazana da kuntatawa da matsin lamba wadanda suke tattare da ayyukan Imam Sadik (a.s) na ilmantarwa wadanda kuma riwayoyi masu yawa na tarihi ke nakalto mana,  sakamakon wannan luran ne da kasancewar mas’alar mai hadari ce. Kazalika muhimmancin da Mansur ya bayar wajen tara mashahuran fukaha’u daga Hijaz da Irak a hedkwatarsa, kamar dai yanda nassoshin tarihi mayawaita suke nunawa, shi ma ya samo asali ne daga wancan lurar da ya yi.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 next