Tafarki Zuwa Gadir Khum



(Suka ce): “Ke nan ba wanda ya shige shi?”

(Ya ce): “E, ba wani mutum da ya zo masa”.

Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana sauraron tattaunawar, sai ya fadi a cikin zuciyarsa: “Alhamdu lillah”. Nutsuwa ta mamaye zuciyarsa.

Tafiya

A lokacin da aka ayyana (zuwan Jagoran hanya), sai ya zo yana janye da rakuma biyu, bayan kwanaki uku da Manzo (S.A.W) ya yi a kogon.

Yasrib (Madina) tana arewa da Makka, amma duk da haka Manzo (S.A.W) ya yi kudu wajen kogon Sauru domin boye tafiya da cikakken sirri: Dan jagora ya yi hanyar kogin maliya, ya kama hanya mafi nisa daga karauka. Tafiyar ta kasance mai wahala, ta dauki kwana bakwai. Annabi yana ratsa mamaleliyar Saharar Tahama a zafi mai kuna, a hanya mai tsanani, hakika ya ketare hadarin, Kuraishu ta kasa komai.

A 12 ga Rabi’ul Awwal ya kai alkaryar Kuba’a a nahiyar yankin Yasrib (Madina) A Kuba’a Annabi (S.A.W) ya yi kwana hudu yana jiran zuwan dan Amminsa, Ali bn Abi Dalib (A.S). Yayin da ranar Juma’a ta zo, Manzo (S.A.W) ya fuskantar da fuskarsa nahiyar Madina, ya kasance dubunnan mazaunan Madina suna sauraron zuwansa.

A wannan lokacin mai ban tsoro, yayin nan ne garuruwa suke canza sunayensu, a 16 ga Rabi’ul Awwal da ya yi daidai da ga watan Yuli 622 miladiyya, Annabi (S.A.W) ya isa Yasrib a lokaci mai dawwamammen tarihi, mutanen Madina kaf sun mike don tarbar karshen Annabawa a tahiri.

’Yan matan Madina suka fito suna wakar farin ciki, suna kallon abin hawan mai hijira (Annabi) yana keta Saniyyatul Wada’a, a wannan lokuta masu cike da buri da farin ciki ne tarihin hijira ya fara, aka kafa tsuron al’ummar Musulunci.

Al’amari Na Biyu



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next