Tafarki Zuwa Gadir Khum



Makka ta kasance gari ne wanda mutanenta azzalumai ne da suka yi shirin kashe mutumin da sama ta aiko domin tseratar da duniya. Sai dai Ali, da jin wannan amsar (cewa Manzo zai tsira), sai bakin cikinsa ya koma farin ciki.

Saurayi (A.S) ya tafi cikin nutsuwa zuwa shimfidar Annabi (S.A.W) ya lulluba da bargonsa yana sauraron takubba su yayyaga namansa, su zubar da jininsa mai tsarki. Ali (A.S) ya yi barci a shimfidar Annabi, yayin da shi kuma (Annabi) ya fuskanci hanyar gudu daga mutanensa ta hanyar Madina.

Hanya Zuwa Yasrib

Matakin Annabi (S.A.W) shi ne ya fuskanta zuwa kudu zuwa Kogon Sauru domin ya buya a can wasu kwanaki, ta yiwu a yi tattalin kayan hawa da tafiya, Kuraishu ta yanke kauna daga kama shi, kamar yadda kwanan Ali (A.S) a kan shimfidarsa ya ba da gudummuwa sosai wajen batar da kama da jinkirta ganewar masu kaidi ga labarin hijirarsa.

A yanayi na sirri kwarai Ali (A.S) ya sayi rakuma biyu ga Annabi (S.A.W) da sahabinsa Abubakar, kamar yadda yarjejeniya ta cika da dan jagoran nan na sahara, wato Abdullah dan Uraikidi. Duk da mutum ne da ya wanzu kan shirkarsa, amma hakika ya kasance mutum ne amintacce da Annabi (S.A.W) ya dogara da shi. Kuraishawa sun fadaka suka dauki matakai masu tsauri, mahaya suka fantsama neman Annabi (S.A.W), aka kuma sanya kyauta mai yawa ga wanda ya kamo shi, ko ya nuna wata alama da za ta sanya kama shi, amma duk da sun samu wasu mutane suna da shaidu masu girma, amma suka samu rashin sa’a wajen samun su.

Hakika Kuraishawa sun natsu cewa lallai zasu kama Muhammad (S.A.W), har ma sun samu labari na wani yanki da ake kokwantonsa. Kai har ma sun kai Kogon Sauru, inda Annabi (S.A.W) da Sahibinsa suka buya, sai ikon Allah ya shiga tsakani don kare Annabin karshe (S.A.W). Dayansu ya hau kan kogo don ya ga abin da yake ciki da wanda ke ciki. Nan da nan sai ya dawo zuwa ’yan uwan tafiyarsa.

“Menene a nan? (Suka ce)

(Ya ce): “Ba komai”.

“Kogo fa?”

“Na ga sakar gizo-gizo a bakinsa, ina ganin ya saka ta tun kafin haihuwar Muhammad (S.A.W). Na ga shekar akwai tattabara biyu a cikinsa da kuma rassan itaciya, sun shiga juna ta yadda ba yadda za a yi wani mutum ya shiga kogon sai ya kawar da ita”.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next