Tafarki Zuwa Gadir Khum



Hanyar Gadir tana da nisa daga babban titi a wannan zamani, saboda rairayin da ya mamaye hanyar karauka a lokutan baya da suka gabata, kamar yadda a yanzu ake ce wa wannan yanki Algurba. Har yanzu akwai wata idaniyar ruwa da take bubbugo da ruwanta daga cikin duwatsu a wani waje mai yalwa.

Saboda samuwar wannan idanwar ruwa ne itacen dabino da itacen arak suka fito a duk wurin, wanda ya bar garin Jidda a kan hanyar nan ta gefen kogin maliya zai isa mararrabar nan ta Juhfa a kusa da garin Rabig daidai da tashar jirgin saman cikin gida na Saudiyya a daman hanya. Daga mararrabar zuwa masallacin mikati wanda aka sabunta gina shi a gefen kusa da kufan wani masallaci dadadde rusasshe zai kai kilomita goma. Daga masallacin mikati zai yiwu a fuskanci Kasrul ulya ta wata hanya wacce take cike da rairayi daidai inda alamomin kufan tsohuwar hanyar hijira suke.

Shi kuma Kasrul Ulya yana kusa da alkaryar nan ta Juhufa ta fuskar hanyar nan da ta yi Madina da garin Rabig. Shi kuma masallacin mikati yana fuskacin hanyar da za ta kai zuwa Makka. Nisan da yake tsakanin masallacin mikati da Kasrul ulya ya kai kilomita biyar, kwararar ruwa da iska duk sun yayimo malalar rairayi da suka yi shingaye na rairayi tsakanin yankunan guda biyu. A wannan yanki akwai tsaunuka na duwatsu da suka iyakance hanyar nan da takan kai zuwa wani wuri mai yalwa inda hanyoyi suka rarraba.

To daga nan zai yiwu a dauki hanyar Guraba wacce da wahala a gane ta saboda yawan mamalelen rairayi. Amma yankin Gadir yana yankin Harra, wanda wuri ne da yake cike da bakaken duwatsu wadanda ba sa karbar shuka, a karshen Harra akwai wannan wuri mai yalwa da fadi, inda idanun ruwan Gadir yake. A wannan wurin Annabi (S.A.W), ya tsaya domin ya isar wa tawagar alhazai da al’ummar musulmi sakon sama na karshe. Wurin mai yalwa yana tsakanin jerarrun duwatsun arewa da na kudu. Idanun ruwan Gadir yana bubbuga daga kusa da gindin duwatsun bangaren kudu, wanda sun fi na Arewa girma sosai,

A daidai kwararon wuraren ne itacen dabino suka tsuro, akwai tsammanin kwarai cewa wadannan itacen sun tsuro ne sakamakon jefar da kwallon dabino da matafiya suka yi a wurin. Yalwar fadin wurin da ruwan Gadir suna jan hankalin matafiya zuwa ga neman hutawa da shan gahawa a wurin.

A kusa da magangaran wajen a bangaren yamma akwai fadama inda ruwa yake bubbuga ya haifar da wata magudana, saboda tsananin kwararar ruwan ne a lokutan ruwan sama ya sanya yanayin yankin yakan canza akai-akai. Wanda yake so ya samu albarkacin wannan wuri inda karshen Annabawa ya tsaya zai yiwu ya iya bi ta hanya biyu ta Juhufa da Rabig.

Hanyar farko tana farawa daga mararrabar hanyar Juhufa daidai filin jirgin saman Rabig inda hanyar matafiya take mai tsayin kilomita tara zuwa alkaryar Juhufa, a wajen akwai wani babban masallaci. Daga Alkaryar hanyar tana karkata dama da nisan kilomita biyu, tana cike da yashi, kuma yanki ne mai cike da duwatsu, to daga karshenta ne filin Gadir yake farawa. Amma hanyar ta biyu tana farawa daga mararrabar hanyar Makka da Madina ta hanyar Rabig. Bayan tafiyar kilomita goma hanyar da take kaiwa zuwa Gadir take yankewa, Daga Rabig zuwa Gadir zai kai kusan kilomita ashirin da shida.

An gina masallacin a wannan wuri mai tsarki, amma yanzu ya rushe kuma ba wata alamarsa sakamakon gudanar ruwa da iska. Ta yiwu masallacin ya kai kusan wannan lokuta zuwa farkon karni na takwas, lokacin da ya rushe ba abin da ya rage sai katangunsa. Dalilin da ya sa aka gano haka shi ne littattafan fikihu da tarihi da abin da ya zo na mustahabbancin yin wasu ayyuka kamar addu’a da salla a cikinsa.

Kuma akwai alamomin da suka zo game da wajen da Annabi ya tsaya a cikinsa, inda ya shelanta wilayar Imam Ali (A.S) a cikin taron al’ummar musulmi, Bakari yana cewa: Wurin yana tsakanin Gadir da idaniyar ruwan, kamar yadda Hamawi ya fadi a cikin Mu’ujamul Buldan, ya kuma iyakanta wurin masallacin. Haka nan an ambace shi a littafin Jawahir, kuma ya yi nuni zuwa ga ragowar kufan garunsa rusassun tare da dogaro da abin da ya zo a Durus na Shahidul Awwal Muhammad bn Makki, amma Ibn Batuta ya yi nuni zuwa ga wucewarsa ta yankin da garuruwan kusa da Juhufa suke ne a tafiyarsa zuwa ga hajjin dakin Allah mai alfarma.

A Musulunci an mustahabbantar da tsayuwa a Gadir Khum da salla a cikinsa da addu’a. Hakika daya daga cikin sahabban Imam Sadik (A.S), an ruwaito daga gare shi cewa ya tafi tare da shi daga Madina zuwa Makka. Yayin da suka isa masallacin, sai ya ce, “Nan ne wurin sawun tafin Manzon Allah (S.A.W) yayin da ya ce “Duk wanda nake Shugabansa, to wannan Ali Shugabansa ne. Ya Ubangiji ka taimaki wanda ya taimaki wanda ya taimake shi, ka ki wanda ya yi gaba da shi, ka tabar da wanda ya ki riko da shugabancinsa”.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next