Tafarki Zuwa Gadir Khum



Hakika mustahabbancin salla a masallacin Gadir ya zo a da yawa daga littafan fikihu, kuma Annabi (S.A.W) ya tsaya a yankin Gadir bayan saukar wahayi, “Ya kai wannan Manzo ka isar da abin da aka saukar daga Ubangijinka, kuma idan ba ka aikata ba, to ba ka isar da sakon sa ba, Allah ne yake kare ka daga mutane”.

Littattafan tarihin sun ambaci cewa hakika Manzon Allah (S.A.W) ya yi umurni da a tsai da karauka domin ya yi huduba mai girma a rana mai tsananin zafi, al’amarin da ya sanya musulmi suna tambayar musabbabin tsayawa a wannan wurin mai tsananin zafi, kuma ya yi huduba yana mai cewa: “Godiya ta tabbata ga Allah, Muna neman taimakonsa, muna imani da shi, muna dogaro da shi, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu, wanda ba mai shiryarwa ga wanda ya batar. Ba mai batarwa ga wanda ya shiryar, ina shaidawa babu abin bautawa sai Allah kuma Muhammad bawansa ne, Manzonsa ne.

Bayan haka, ya ku mutane! Hakika Mai tausayi, Mai sani (S.W.T) ya ba ni labari cewa ba wani Annabi da aka rayar sai kwatankwacin rabin rayuwar wanda yake gabaninsa, kuma ni an kusa kirana in amsa, ni abin tambaya ne, ku ma haka. Me za ku ce?”

Sai suka ce: “Mun shaida ka isar da sako, ka yi nasiha, ka yi kokari, Allah ya saka maka da alheri”.

Sai ya ce: “Shin ba ku shaida ba abin bautawa da gaskiya, sai Allah ba, kuma hakika Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne ba, aljannarsa gaskiya ce, wutarsa gaskiya ce, mutuwa gaskiya ce, kuma tashin alkiyama mai zuwa ne ba kokwanto a cikinta, kuma Allah (S.W.T) yana tashin na cikin kaburbura”?.

Suka ce, “E, mun shaida da haka”.

Sannan ya ce: “Allah ka shaida” kuma ya ce: “Ya ku mutane! Shin kuna ji na”?.

Suka ce, “E”.

Sai ya ce: “Ni zan gabace ku tafki (alkausar), kuma ku zaku zo min a wajen tafkin, fadinsa ya kai tsakanin Sana’a da Busra, a cikinsa akwai kofuna adadin taurari, ku duba ku gani, yaya za ku maye (bi) nauyaya biyu, wato littafin Allah da Ahlin gidana bayana”!.

Sai wani ya yi kira da murya madaukakiya, “menene nauyaya biyu ya Manzon Allah?”.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next