Tafarki Zuwa Gadir Khum



Haka nan imanin wannan saurayi yake, wanda bai san wani Shugaba ba banda Muhammad (S.A.W). Muhammad din da ya bude idanunsa a kan kofofin haske a tuddan duwatsun Hira. Tawaga ta kutsa cikin rairayi, yana tafiya sannu-sannu, a tare da shi akwai Fadimomi: Fadima ’yar Asad, da Fadima ’yar Muhammad, da Fadima ’yar Hamza, da Fadima ’yar Zubair.

A wani wuri “Ziduwa” ababen zalunta suka saurari zuwan Ali (A.S) don ya tseratar da su daga garin da al’ummarta suke azzalumai, suka keta hanyar kwarurruka da kwazazzabai da  babu komai sai shudiyar sama da farin rairayi.

Ali (A.S) ya san abubuwa da yawa, tun kafin shekaru ashirin ne yake tare da zababben Allah (S.A.W), ba kawai yana tare da shi bane, sai dai ya narke a cikinsa ne narkewa. Shi ya sa shi ya san sirrin duniya (halitta). Abu guda ne Ali (A.S) bai san shi ba faufau, wato; tsoro, hakika mutum ya gajiya gaban surkukiyar mutuwa karshen rayuwa, shin shi ne karshe ko farko?


[1] - Surar Ahzab\ aya: 33

[2] - Sahihan Littattafai Da Masanid

Amma Ali (A.S) ya gano makamar dawwama, ya rinjayi mutuwa ba sau daya ba, ba sau biyu ba, amma mutuwa tana gudunsa, tana guje masa duk sadda ya so rungumar ta. Ya lulluba a cikin bargon Annabi (S.A.W), ya runtse idanunsa a shimfidar da kanshin aljannar Firdausi ya mamaye shi, yana mai ba da ransa fansa ga karshen Annabawa a tarihin dan Adam.

Idan Isma’il ya mika wuya ga Allah, lallai ya san babansa zai yanka shi a sannu-sannu ne, sai dai Imam Ali (A.S) ya runtse idanunsa don ya bude su a kan gomomin takubba masu guba. Mala’iku sun so kansu wajen gogoriyon rayuwa, Jibril (A.S) bai fanshi Mika’ilu ba (A.S), kowannensu ya zabi rayuwar, amma sai ga shi wannan saurayi mai suna Ali da ubangiji mai iko ya kare shi, yana mai karya bangon mutuwa, ya zabi mutuwa dan’uwansa Manzon rahama ya rayu.

Tawaga tana tafiya har ta kai kusa da “Rajnan”, sai aka cim mata, sai ga mahaya doki takwas sun bijiro musu suna son su mayar da hannun agogo baya. A nan ne aka yi wa yankin nan na Larabawa bazata da “Zulfikar”. Takwas din nan suna son su mayar da tawagar zuwa Makka, zuwa alkaryar da mutanenta azzalumai ne, idanu suna cike da hikidu da mugun kulli. Wani mahayin doki cikinsu a lokacin ba a san waye Ali ba, ya ce:

“Kai mayaudari, kana tsammanin za ka tsira da mata? koma don gidanku!” Tir da wannan magana da ya gaya wa Ali.

Ali ya amsa da sabati kamar dutsen Hira, “In ban koma ba fa?”.

Suka ce: “Ko ka ki, ko ka so”.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next