Tafarki Zuwa Gadir Khum



Idanun Fadima (A.S) suna yawo tsakanin taurari suna kallon sasannin sama inda babanta ya yi tafiyar isra’i da mi’iraji a kan Buraka. Idanun Fadima (A.S) ba su gushe ba suna kallon taurari, fuskarta tana haskakawa kamar tauraron da ya sauko kasa, wata ya bayyana a karshen dare. A lokacin Fadima (A.S) ta lumfasa tana munajati da Ubangijinta.

“Kai ne mai wanzuwa, komai mai bacewa ne, taurari wata... Fararen rayuka suna fuskantar ka, ba ruwansu da kayoyin da ke kan hanya a sahara, koda kuwa ba su da takalma, kai kadai ne gaskiya. Ya Ubangiji kai ne hasken idanuna da farin cikin zuciyata, ka bar ni in kutsa wa malakutinka in yi tasbihi, in kewaya tare da taurari a gefen Al’arshinka, kai kadai ne hakika, waninka wahami ne. Kai kadai ne mabubbugar rayuwa, waninka sururi ne da mai jin kishirwa yake tsammanin ruwa ne”.

A Kuba’a Jibril (A.S) ya sauka yana dauke da kalmomin sama zuwa ga mutumin da ya gudu daga uwar alkaryu (Makka) yana ba shi labarin matafiya da ’yarsa, da matar da ta rene shi, da saurayin da ya rena a dakinsa, wanda yayin da ya girma ya tsaya a gefensa yana kare shi iyakar karfinsa.

A nan ne fa mafarkin nan na wahayi ya tabbata, farfajiyar Kuba’a ta yi yalwa, yayin da Annabi (S.A.W) ya gina masallacin farko a Musulunci. “Wadanda suke ambaton Allah a tsaye da kuma tunani a cikin halittar sammai da kasa (suna cewa): Ya Ubangijinmu ba ka halicci wannan don wasa ba, tsarki ya tabbata gare ka, ka kiyashe mu azabar wuta. Sai Ubangijinsu ya amsa musu cewa ni ba na tozarta ladan aikin mai aiki, namiji ko mace, sashenku daga sashe yake, wadanda suka yi hijira daga gidajensu aka cutar da su a tafarkina, suka yi yaki aka kashe su, zan shafe kurakuransu, kuma in shigar da su aljanna koramu suna gudana ta karkashinta, sakamako daga wajen Allah, Allah a wajansa akwai kyakkyawan sakamako”.

Annabi (S.A.W) ya kasance yana sauraron isowar tawagar matafiya da ’yarsa da mai renonsa suke ciki, kuma kalmomin da Jibril (A.S) ya gaya masa ba sa gushewa cikin tunaninsa, yana kallon nesa, amma ba komai sai yashi. Da an kaddarawa wani yana Kuba’a a wannan lokaci da (ya ga abin mamaki), ya ga wani mutum wanda ya kai shekara hamsin, shi ba dogo ba, ba gajere ba, matsakaici, (hakika an sanya alheri duk a cikin tsakaitawa), mai farin fuska, mai fari tas, an cakuda shi da jaja mai sauki (ta yiyu sakamakon rana ta doke shi ne), mai yawan gashi zai kai bayan kunnensa, ya kusa ya hau kafadunsa, mai yalwar goshi, mai lankwasassun gira kamar wata (jinjirin wata biyu), idanunsa masu haske ne, masu fadi, mai madaukakin karan hanci, hakoransa kamar lu’ulu’u ne da aka daddasa, idan yana tafiya yana tafiya da sauki, takunsa makusanta ne kamar kwale-kwale da ya yo gangara.

Annabi (S.A.W) ya tsaya yana tunanin sahara mai nisan gani yana sauraron masoyan da ya bar su a wani lokaci na dare, kurayen Makka sun kewaye shi. Dare ya mamaye sahara, Annabi (S.A.W) ya koma hayin Bani Saham, a fuskarsa akwai bakin ciki kamar bakin cikin annabi Adam ranar da yake binciken Hawwa a bayan kasa.

Matafiyan (masu hijira) sun isa da aminci, Uban (S.A.W) ya tattaka domin haduwa da tarbar ’yarsa abar tunawarsa daga Hadiza (A.S), Hadizar da ta tafi ta bar shi shi kadai. ‘Yar ta rungume Babanta, ta dulmiya cikin tunaninsa, idanunta cike da hawaye, hawayen farin ciki da rahma. Mamakin girman wahalar da Muhammad ya sha! Mamakin girman wahalar da Annabawa suka sha!

Ta yiwu ya ba da mamaki kwarai ga wasu mata su ga mutumin da ya haura shekara hamsin ya zama kwatankwacin misali na dan yaro a karkashin renon babarsa. Yana mai niyyar sanya haddi ga tambayoyi da zasu yadu cikin mutane, yana mai cewa da ita: “Fadima (A.S) Babar Babanta ce”. Fadimar da take a kan sha ukunta, amma sai ga ta ta koma Uwa ga mafi girman Annabawa (A.S). Da kuma fadinsa: “Fadima tsoka ce daga jikina”.

Muhammad (S.A.W) ya kalli idanun ’yarsa da suka zama suna binciken saurayin da ya sayar da ransa saboda Allah a cikinsu, amsar da ke idanunta shi ne: Ga shi can ya Baba, shi ne... wanda kafafunsa suka tsattsage, jini ya zubo ta cikinsu da sukan kaya da zafin rana da wahalar sahara, ba shi da taguwa ko rakumi. Idanun Annabi (S.A.W) suka amsa cewa: Ashe dan’uwana ne take so! Sai Muhammad (S.A.W) ya tafi don haduwa da dan’uwansa mai hijira, shi kuwa saurayi ya tashi domin haduwa da Manzon sama (S.A.W) yana mai mancewa da zoginsa da wahalhalunsa.

Annabi (S.A.W) ya sanya tafinsa mai kanshin Rahikul mahtum na Annabta ya shafa duga-dugan saurayi mai hijira kamar uwa tana shafa kan danta don ya lallasu ya yi barci.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next