Tafarki Zuwa Gadir Khum



Fararrun Abubuwa A Hanyar Hajjin Karshe

Al’amari Na Farko

A watan Zul ka’ada, a shekara ta goma hijira, Annabi (S.A.W) ya shelanta niyyar zuwa hajjin dakin Allah (S.W.T). Iskar sahara ta dauki labaran farin ciki. Sai ga kabilun Larabawa suna ta kwararowa zuwa Madina don su shiga karkashin tutar karshen Annabawa a tarihi, gomomin dubunnai suka tafi suna masu barin alkaryunsu da biranensu da hayoyin kabilunsu.

Ashirin da biyar ga wannan wata karaukoki suka nufi Makka (Wajen son kowa), Sahara ta ga taron farko mafi girma da ya kai mutum dubu dari suna masu tafiya cikin sauki zuwa ga dakin da Ibrahim da Isma’il (A.S) suka gina shi. A biyar ga Zulhajji mai alfarma, Annabi ya shiga Makka daga Babus Salam, ya yi dawafi gefen tsohon daki (Ka’aba) sau bakwai, sannan ya tafi Safa da Marwa, yana mai koyi da ayar Kur’ani “Lallai Safa da Marwa yana daga cikin alamomin (addinin) Allah”.

Ya yi sa’ayi tsakanin duwatsun biyu a motsi da yake tunatarwa game da babar Isma’il (A.S) yayin da take binciken digon ruwan sha ga danta Isma’il (A.S), ya hau dutsen Safa ya kalli Ka’aba mai girma, ya shelanta karewar bautar gunki.

“Ba abin bauta sai Allah daya, Ba shi da abokin tarayya, Mulki da godiya sun tabbata a gare shi. Shi mai iko ne a kan komai, Ba abin bauta sai Allah, ya cika alkawarinsa, ya taimaki bawansa, ya rusa runduna shi kadai”.

A Arfa Annabi (S.A.W) ya tsaya yana mai huduba, ya yada al’adun Musulunci tsakanin musulmi, yana mai albishir da bankwana na aminci. Yana mai cewa: “Ya ku mutane! Ku ji daga gare ni, ta yiwu ba zan hadu da ku bayan wannan shekarar ba a wannan wuri nawa, lallai jininku da dukiyarku haramun ne har ku hadu da Ubangijinku kamar haramcin ranarku wannan”.

Sannan ya shelantar da wurgi da kabilanci da kuma wajabta girmama mutum: “Ya ku mutane! hakika Ubangijinku daya yake, kuma babanku daya ne, dukkanku daga Adam (A.S) kuke, shi kuwa Adam daga kasa yake, Kuma mafi girmanku a wajen Allah (S.W.T) shi ne mafi tsoron ku ga Allah, balarabe ba shi da wani fifiko a kan ba’ajame sai da takawa”.

Sannan ya wuce yana mai kafa sababbin dokoki da aminci da soyayya da kaunar juna zai zama a cikinsa. Ya ce: “Duk wanda yake da amana, to ya ba da ita zuwa ga wanda ya ba shi amana. Kuma ribar jahiliyya babu shi, kuma farkon riba da zan fara saryar da shi shi ne ribar Ammina Abbas dan Abdulmudallib, kan dukiyarku yana gare ku, ba ku zalunta ba, ba a zalunce ku ba. Kuma bin jinin jahiliyya babu shi, kuma farkon jinin da zan saryar shi ne jinin Amir dan Rabi’a dan Haris dan Abdulmudallib”, yana mai kare bayaninsa da cewa: “Na isar! Allah ka shaida!”

Annabi bai manta bayanin hakika mai girma ba ta hanyar da zasu bi bayansa (S.A.W). Ya ce “Ya ku mutane! Lallai muminai ’yan uwa ne, dukiyar dan’uwa musulmi ba ta halatta gun dan’uwansa musulmi sai da yardarsa. Kada ku koma kafirai bayana sashenku yana dukan (saran) wuyan sashe. Kuma hakika ni na bar muku abin da idan kun yi riko da shi ba za ku taba bata ba bayana har abada - littafin Allah da Ahlin gidana”.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next