Tafarki Zuwa Gadir Khum



Hafiz Muhammad Sa'id Kano Nigeria

hfazah@yahoo.com

Khurdad 1381 H.SH, Mayu 2002 M

Gabatarwar Mawallafi

A tarihin Musulunci akwai abubuwan da suka damfara da bayanin sunaye madaukaka a tarihi, sunayen mazaje ne gwaraza da suka cika wa Allah alkawarin da suka dauka da kuma mataye muminai. Da sunayen wuraren da ke can kasar wahayi da duk wani wuri da Annabi ya tsaya a wurin, kamar kogon Hira wanda ya ga hudowar haske, hasken ruhi mai tsarki. Zuwa Zazar Abi Dalib, zuwa gidan Arkam, zuwa kogon Sauru, zuwa idaniyar ruwa ta Badar, zuwa dutsen Uhud da bishiyar Ridwan, zuwa Hudaibiyya da Fadak zuwa… Gadir Khum.

A cikin wannan waje, a inda idanun Gadir ke kwarara, inda Annabi (S.A.W) ya tsaya yana mai isar da sakon Ubangijinsa a sakon karshe na sama. Na’am wannan waje, waje ne mai tsarki, inda Jibril (A.S) ya sauka dauke da sakon sama “Ya kai wannan Manzo ka isar da sakon da aka saukar gare ka daga ubangijinka! Idan ba ka yi haka ba, to ba ka isar da sakonsa ba!” Annabi ya tsaya, tawagar alhazai ta tsaya, sannan ya shelanta a cikin wannan taron jama’a “Duk wanda nake Shugabansa, to wannan Ali Shugabansa ne”.

A wannan lokaci na tarihi a zamani an sami bayyanar abubuwa na farin ciki domin su dawwamar da wannan rana ta goma ga Zulhajji, shekara ta goma da hijira domin ya zama idi mai tarihi. Wannan gabatarwa mun kawo ta ne domin ta share fagen bayanin Gadir a tarihin rayuwar musulunci bayan haskakawar tarihinmu mai girma.

Kamal Assayyid

Tafarki Zuwa Gadir Khum

A tsakanin hanyar Makka mai girma abar girmamawa da Madina mai haske abar haskakawa, a kusa da Juhufa, akwai wani yanki wai shi Gadir Khum. Gadir ya kasance a hanyar matafiya ne, Manzon Allah (S.A.W) ya taba wucewa ta nan a lokacin hijirarsa mai tarihi a watan Rabi’ul Awwal shekarar 622 miladiyya, kamar yadda ya tsaya a 18 Zul hajji shekara ta goma hijira a lokacin dawowarsa daga hajjin bankwana. Ta haka ne wannan wuri ya shiga cikin tarihin Musulunci mai girma.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next