Tafarki Zuwa Gadir Khum



A cikin duhun dare ne haduwar ta wakana, Akaba wuri ne kusa da Makka. Hanyar tsira da kubuta ta bude, Annabi (S.A.W) ya dawo alkaryarsa yana yi wa mabiyansa albishir da cewa: “Allah ya ba ku ’yan uwa da garin da zaku zauna ku debe kewa a cikinsa”.

Haka nan sabon shafin rayuwar Musulunci ya fara a wadannan kwanaki masu cike da wahalhalu da firgici da tsoro da buri. An ga mutane suna gudu suna barin garinsu da aka haife su suka taso a ciki.

Kuraishu da tsaurin kanta ta kasa gamawa da wannan al’amari mai hadari a gun ta. Al’ummar Makka ta fara girgiza ana barin gumaka, maslaharta tana raurawa.

Makirci

Abu Jahal, da Abu Sufyan, da Umayya, da dukkan manyan Kuraishawa suka ga mafificiyar hanyar mafita shi ne gamawa da Manzo da hutawa daga gare shi. Tunda rabe-raben kabilu da kuma matsayin Bani Hashim a al’umma da kare Manzo da suke yi tsayin shekaru daga kisa. To idan kabilu da yawa suka yi tarayya a kashe shi, wannan zai sanya Bani Hashim su kasa daukar fansa, su yarda da diyya. Haka nan ran Abu Jahal ta kitsa masa don makirci.

Makirci ya kai hadarin da sai da Jibril (A.S) ya sauka daga sama da wannan aya. “Kuma yayin da kafirai suke kulla makirci a gareka domin su tsare ka ko su kashe ka ko su kore ka, suna makirci, Allah shi ne fiyayyen mai (raddi ga) kulla makirci”.

Dare ya yi a Makka, taurari sun bayyana, dare na cike da zukata masu boye gaba ga Manzon Allah (S.A.W) daga nesa. Abu Jahal na sanye da abayarsa, yana mai takama da tunaninsa, yana ganin cewa Makka za ta karfafa da tunaninsa, ya zama mutumin tarihinta (Gwarzo), dabararsa ta zama mafita kuma abin fada.

Fansa

A cikin wannan lokaci mai tashin hankali kuma ana dab da zartar da shirin da aka kulla, sai gwarzon saurayin nan na Musulunci a tarihi, a daya daga cikin irin sadaukarwarsa ya fanshi Manzo (S.A.W) da ransa. Wannan saurayi shi ne Imam Ali (A.S), hakika yana daga jarumtaka mazaje su shiga fagen fama suna yaki har mutuwa, amma mutum ya kutsa wa mutuwa karkashin sukan takubba da masu da zabinsa, wannan abu ne wanda alkalami duk yadda ya kai bayani da zurfi wajen bayyanawa bai isa ya iya kawo hakikanin wannan jaruntaka ba.

Ali ya sunkuya yana sauraron maganar mutumin da ya rayu da shi sama da shekara ashirin. Ya ce: Shin za ka tsira ya Manzon Allah idan na fanshe ka da raina? Sai ya ce, “E mana, haka Ubangijina ya yi min alkawari”. Ali, da ya kasance mai bakin ciki, amma da jin haka, sai zuciyarsa ta yi fari.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next