Tafarki Zuwa Gadir Khum



Mutuwa da rayuwa sun zama ala-kakai a rayuwar mutum. dan hakin da aka raina zai tsone ido fa. Ga wanda ke son rayuwa, wace hanya zai bi? Hanyar rayuwa ko mutuwa? duba mana ku ga gida mai girma a Makka ya yi shekara goma sha uku da saukar Jibril (A.S) a kogon Hira.

Mushrikan Makka suka ga akwai hadari, suna ganin ’ya’yan Makka suna gudu da addininsu, suna gudu arewa zuwa Madina, Allah ya tashi mutane don taimakon sakon sama. Hijira ta yawaita har ta washe unguwa gaba dayanta, Kuraishu suka ga matakinsu bai kai ga nasara ba, kullum hadari yana karuwa. Abu Jahal ya motsa don ya sanya mataki na jahannamanci don gamawa da Muhammad (S.A.W) har abada.

Jibril (A.S) ya sauka yana mai kunyata da bata matakin Shedan na bice hasken da ya haskaka a dutsen Hira zai haskaka duniya gaba daya. “(Tuna) Yayin da wadanda suka kafirta suke makirci don su tsare ka ko su kashe ka ko su fitar da kai, suna makirci, Allah yana makirci, Allah shi ne fiyayyen masu iya (sakamakon) makirci”.

A wannan lokaci ne mai tarihi daya daga mafi girman fansar da kai ta faru a tarihin dan Adam. Duk irin tunanin mutum ba zai iya suranta yanayi na wannan saurayi dan shekara ashirin da uku, yana shiga gaba don rungumar mutuwa ba. Abubuwa suka faru akai-akai, Kuraishu ta saka mafi girman makircinta kamar yadda gizo-gizo yake saka gidan da yake shi ne mafi raunin gidaje. Annabi (S.A.W) ya kira dan Amminsa, masoyi, ya nuna masa kaidinsu, ya zama abin da yake so daga Ali (A.S) shi ne ya kwana a shimfidar Annabi (S.A.W), amma abin da ya zama burin Ali dan Abi Dalib shi ne ciran Manzo don haka ya tambaya, “Shin za ka kubuta ya Manzon Allah in na fanshe ka da raina?”

“E, haka Allah ya yi mini alkawari”. Sai ga farin ciki yana bayyana a fuskar Ali (A.S). Ya gabata wajen shimfidar Annabi (S.A.W) don ya kwanta ya yi barci da aminci da natsuwa. Yayin da idanun miyagun (mutane) arba’in suna sauraro a cikin duhu (don kashe Manzo), lokaci ya ja Manzon Allah (S.A.W) ya sulale wajen gida ya fuskanci kudu zuwa kogon Saura.

Miyagu suka kewaye gidan Manzon Allah da takubba masu kyalli, a ketowar farko na alfijir fuj’atan ai Ali ne! ya tashi daga shimfidarsa: Manzo ya riga ya kubuta!. A lokacin safiyar farko Makka ta ga wani sabon yanayi mara dadi. Ashe Manzon da Allah ya aiko domin ya cika kasa da haske ya gudu, mahaya dawakai suna ta bincike kowane waje. Kuraishu ta sa kyauta mai yawa ga wanda ya zo da Muhammad (S.A.W) a raye ko a mace, ko ya bayar da wata alama da za ta sa a kama shi.

Ali (A.S) ya zauna a Makka kwanaki yana shelantawa a kwarin Makka cewa, “Duk wanda yake da wata amana a wajen Muhammad (S.A.W) ya zo mu ba shi kayansa”.

Wasika Daga Kuba’a

Manzo (S.A.W) ya isa Kuba’a ya sauke kayansa a can, daga nan ya aika da wasika zuwa ga dan Amminsa yana umurtar sa da ya zo. Abu Wakid Allaisi ya tafi Makka ya ba wa Ali (A.S) wasika. Wai menene ya sa wannan nacewar don sauraron zuwan Ali (A.S), bai shiga Madina ba har sai da Ali (A.S) ya zo?

Lallai tarihin hijira ya ba da labarin sauraron wannan lokaci mai zafi da tsanani don haduwar Muhammad da Ali (A.S), lallai a cikin ruhin Ali (A.S) akwai sirri mai ban mamaki, yayin da hakika take bayyana a zatin mutum, ta sanya duk abin da yake tattare da shi ya damfaru da haske wanda ba daga rana ko wata yake ba, sai dai haske ne wanda yake daga tsakatsakin sammai.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next