Tafarki Zuwa Gadir Khum



Sai Junahu ya kawo wa taguwa hari, don ya mai da ita.

Sai Ali (A.S) ya tare shi.

Ya kawo sara, Ali (A.S) ya kare ta.

Ya kuma sare shi, sara mai tsage mutum, ya kuma gama da shi.

Saura suka ja da baya.

Lallai abin ya dimauta su, ba su taba ganin sara kamar haka ba a rayuwarsu. Dayansu ya daga murya, ya ga saurayi yana shiri don kawo hari: “Ka kame kanka daga barin mu, ya dan Abi Dalib”.

Ali (A.S) ya fada da karfi: “Ni mai tafiya ne wajen dan’uwana kuma dan Ammina Manzon Allah (S.A.W)”.

Tawaga ta tafi hanyar Yasrib, Manzon Allah bai gushe ba, yana sauraro a Kuba’a. A 16 ga Rabi’ul Auwal ne, wanda ya yi daidai da 20 ga Yuli 622 na miladiyya tawagar tarihin hijira ta isa garin Yasrib. Jama’ar musulmi ta cika a Saniyyatul Wada’ tana jiran isowar karshen Annabawa a tarihin dan Adam.

Al’amari Na Uku

Sama tana cike da taurari ababen damfarawa, tana walkiya daga nesa kamar lu’ulu’u abin yayyadawa, Muhajirun sun sauka a Rajnan, Ali (A.S) ya sunkuya yana magani ga kafafunsa, da saboda tafiyar daruruwan milamilai sun tsattsage. Taguwowi sun durkusa a kan yashi suna lumfasawa daidai suna jin kanshin gari nan kusa.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next