Tafarki Zuwa Gadir Khum



Annabi (S.A.W) a cike da idanu masu hawaye don farin ciki, ya ce da Hasan, “Ba ka gushe ba da taimakon Ruhul Kuds matukar ka taimake mu da harshenka”.

Sahabbai suka taso suna masu yi wa Ali (A.S) gaisuwa da barka suna cewa: “Barka! Barka! gare ka ya Ali. Ka zama Shugabanmu, Shugaban kuma dukkan mumini da mumina. Ranar 18 ga Zulhajji ta zama ranar idi da farin ciki, kuma hakika addini ya kammala, ni’ima ta cika”.

Al’amari Na Biyu

Manzon Allah (S.A.W) ya tsaya ranar suka a Hajjatul Wada yana mai huduba. “Amma bayan haka, ya ku mutane! Ku ji daga gare ni abin da zan bayyana muku. Ni ban sani ba ko ta yiwu in hadu da ku bayan wannan shekara tawa a matsayina wannan, lallai jininku da dukiyarku haramun ne a kanku har ku hadu da Ubangijinku kamar (haramcin) alfarmar ranarku wannan, a watanku wannan, a garinku wannan”.

“Ya ku mutane! lallai muminai ’yan uwan juna ne, bai halatta ba ga wani mutum ya ci dukiyar dan’uwansa sai da son ransa. Kada ku koma kafirai bayana, sashenku yana dukan sashe. Lallai ni na bar muku abin da in kun yi riko da shi ba za ku taba bata ba bayana har abada: Littafin Allah da Ahlin gidana…”

Aikin hajji ya kare, Annabi (S.A.W) ya koma Makka da wanda ke tare da shi, su dubu dari ko sama da haka. Kuma tarihi ya nuna cewa, ranar goma 18 ga zulhijja na shekara ta goma hijira ne.

Tawagar Alhazai tana keta fagage, rana ta take a sama, ta bude kamar tana huruwa da wuta. Tawaga na isa wani wuri kusa da Juhufa a mararrabar hanyoyi, sai ga sako ya zo wa Annabi (S.A.W) yana kan taguwarsa kuswa, Jibril (A.S) ya sauko yana mai dauke da sakon sama. Annabi ya tsaya yana mai sauraron sakon sama. “Ya kai wannan Annabi! ka isar da sakon da aka saukar maka daga Ubangijinka, in ba ka yi ba, to ba ka isar da sakonsa ba, kuma Allah ne yake kare ka daga mutane”.

Gomomin dubunnai sun tsaya suna tambayar sirrin tsayawar Annabi (S.A.W) a wannan wuri mai tsananin zafi. Sai wasu sashen sahabbai suka hanzarta suka yi wa Annabi (S.A.W) wani tudu, don yana da wasu sakonin da zai isar da ita ga gomomin dubunnan sahabbansa da al’ummu masu zuwa. Kalmomin godiya da yabo da suke fita daga bakin karshen Annabawa (S.A.W), Ali (A.S) ya kasance a tsaye kusa da mutumin da ya rene shi yana yaro, ya sanar da shi yadda zai rayu.

Annabi ya yi bayani, gomomin dubbunai suna tsinkayo a gare shi, ya ce: “Shin ba ni ne mafi cancantar muminai daga kawukansu ba”? Sai ga amsa daga gomomin dubunnan saututtuka: “E, ya Manzon Allah!!”

Ya riki hannun Ali (A.S) ya daga sama, yana mai cewa: “Duk wanda nake Shugabansa, Ali Shugabansa ne. Annabi ya daga hannunsa zuwa sama, ya ce: “Ya Ubangiji ka jibanci lamarin wanda ya taimake shi, ka tabar da wanda ya ki shi, ka taimaki wanda ya taimake shi, ka tozarta wanda ya ki taimakon sa”.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next