Tafarki Zuwa Gadir Khum



Sai Jibril (A.S) ya sauka yana mai albishir ga Muhammad (S.A.W) cewa; ya bayar da wajibinsa na isar da sako. Lokaci ya yi da zai huta, hakika addini ya cika, ni’ima ta kammala, kuma godiya ta tabbata ga Ubangijin talikai. Goshinsa yana sheki, ga gumi… kwayoyin digon gumi suna zuba kamar dige-digen yayyafi, ga sakon wahayi na sama ya mamaye zukata da farin ciki maras misali, wanda ya cika duniya a tarihin dan Adam, “A yau na kammala muku addini, kuma na cika ni’imata a gare ku, na yardar muku Musulunci shi ne addini”.

Al’amari Na Uku

Kwana da kwanaki… Annabi (S.A.W) ya tafi hajji, sakon Allah ya zabi ya kasance a Gadir Khum, a kan hanyar komowa ne Jibril (A.S) ya sauka: “Ya kai wannan Manzo (S.A.W) ka isar da abin da aka saukar maka daga Ubangijinka, idan ba ka aikata ba, to ba ka isar da sakon sa ba”.

“Mutane fa”?

“Allah ne zai kare ka daga mutane”.

Ga rairayi yana kunkuna da zafin da ba za a iya daukewa ba, Annabi (S.A.W) ya tsaya, mutane dubu dari ko sama da haka suka tsaya tare da shi, ga alamomin tambaya suna bayyana a fusaku. Tarihi ya tsaya yana sauraron abin da karshen Annabawa zai ce. Ya ce: “Shin ba nine mafi cancantar musulmi fiye ga kawukansu ba? suka ce: E, ya Manzon Allah (S.A.W)”. Sai ya ce: “Duk wanda nake shugabansa, to wannan Ali (A.S) shugabansa ne… ya ku mutane za ku zo min wajen tafki, ni kuma zan tambaye ku game da nauyayan alkawura biyu”.

Suka ce:- “Menene nauyaya biyu, ya Annabin Allah (S.A.W)?”

Ya ce, “Littafin Allah da Ahlin gidana (A.S)”.

Tawagar alhazai na hajji mafi girma tana shirin komawa zuwa garuruwansu, ga mutane suna shiga addinin Allah, jama’a-jama’a, Jibril (A.S) ya sauka yana karanta wa Manzon Allah (S.A.W) ayar karshen sakon sama, “A yau ne na kammala muku addininku gare ku, na cika ni’imata a gare ku, na yardar muku da musulunci shi ne addini”. Annabi (S.A.W) ya san cewa aikinsa ya kare a bayan kasa, lokaci ya yi da zai huta sai dai…

Masdarorin Madogarar Wannan Littafin:



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 next