Mene ne Auren Mutu'a



"Sannan abinda ya sameku na daga Musiba, to daga abinda kuka aikatane da kanku, (Ubangiji) kuwa yana yafe yawa-yawan (zunubai)"

Don haka kasantuwar Allah mai Adalci ya tanadarwa Al'umar Annabi Muhammadu (Sallallahu alaiHi wa AliHi) auren Mutu'a don kada su afkawa SabonSa.

YADDA AKE YIN AUREN MUTU'A

ABU NA FARKO

Kamar yadda muka samu kenan wannan auren na Mutu'a ingantacce ne da Nassin Kur'ani mai Tsarki da dimbin Nassosi daga Maganganun Manzon Allah (Sallallahu alaiHi wa AliHi), kamar yadda ya gabata na daga hujjoji a baya kadan. To haka nan Mabiya Mazhabin Ahlul-Baiti (Alaihiums-salam) ke kan wannan halasci da bin sa har abada.

ABU NA BIYU

Auren Mutu'a shima aurene da yake dauke da ka'idoji da hukunce-hukunce kamar dai auren Da'imi, illa wasu 'yan bambamce-bambamce dake tsakanin su.

Kamar yadda Babban Malamin Fikhu na Mazahabin Ahlul-Baiti (Alahiums-salam) Al-Allamah Al-Hilliy ya kawo a cikin litttafinsa na Tahrirul-Ahkam, Mujalladi na (3) shafi na (500) yace:

Wajen daura auren Mutu'a babu makawa daga "Al'iijab" wato kaddamar da neman auren. Kuma ana yinsa ne kamar haka:

"زَوَّجْتُكِ أو أَنْكَحْتُكِ أو مَتَّعْتُكِ مُدَّةِ كَذَا بِمَهْرِ كَذَا"

Shine:

(Zawwajtuki, ko Ankahtuki, ko Matta'tuki muddati kaza bi Mahri kaza)



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 next