Jagorancin Imam Sadik (a.s)



1.Akwai wata tsararrar alaka ta tunani da ta abin da ya shafi dukiya tsakanin imamai (a.s) da mabiyansu, kuma an kasance ana daukar dukiyoyi daga sassa dabam dabam na duniya ana kaiwa Madina kazalika da tambayoyin addini mayawaita.

2.Fadadar fagen da ke wilaya ga mutanen gidan Manzo (s.a.w.a) musamman a yankunan duniyar musulunci wadanda suke masu saurin daukar dumi.

3.Tattaruwar jama’a masana hadisi da maruwaita Kurasanawa da Sistanawa da Kufawa da Basarawa da Yamanawa da Misrawa gaban Imam (a.s).

Shin wannan al’amari wanda  sashensa yake munasaba da sajewa da sashe ya faru ne kwatsam ba tare da an shirya shi ba?

Wajibi ne mu yi kari da cewa wannan al’amari ya tabbata ne karkashin ikon siyasa wanda ya yi da gaske wajen watsi hatta da sunan Ali (a.s)  kai da ma zagin Ali a kan mimbarori da wanzar da nau’o’in dira da razanarwa kan mabiyansa. To a irin wannan halin, yaya aka iya samar da mabiya  mayawaita masu wilaya ga Ahlulbaiti  daga cikin talakawa suna taka dubban  milamilai saboda su kai kasar Hijaz da birnin Madina da zimmar daukar karatu gaban imaman Ahlulbaiti (a.s) da kuma koyon tunanin musulunci a kan rayuwar dai-daiku da ta jama’a da kuma tattaunawa da su kan batutuwa mayawaita da kuma mas’alolin tawaye wa yanayin barna da fasadi, ko kuma kamar yanda riwayoyi suke kiran al’amarin-mas’alolin ‘tsayawa’ da ‘ficewa’ daga da’a ga azzalumai )?!!

Idan da ace masu kiran Ahlulbaiti suna takaita bayanansu ne kan ilmin imamai (a.s) da zuhudunsu, to me ya sa tattaunawar wadannan mabiyan a kullum take kan batun tawaye ta hanyar daukar makami? Shin wannan baya nuni da samuwar  wani tsararren shirin sadarwa saboda kira zuwa imamancin  Ahlulbaiti (a.s) da cikakkiyar ma’anar imamanci, watau tsrin tunani da na siyasa?

A nan tambaya za ta zo kan cewa dalilin kawaicin tarihi dangane da samuwar irin wannan tsararren  shirin sadarwa a kiran Ahlulbaiti (a.s). Shin mene ne ya sa tarihi bai ambaci komai kan wannan batu a fayyace ba? Amsa ita ce abin nan da muka yi nuni da shi a baya. Ta yiwu  sahabban imamai sun lizimci ka’idar nan ta  hikima wajen haraka wanda aka sani da takiyya, wanda take ba ta  bada duk wani bare a tsarin imama damar kutsa kai. Haka kuma mai yiwuwa ne tarihi bai ce komai ba saboda rashin kaiwa harakar jihadi ta shi’a ga tabbatar da manufofinta da karbar ragamar mulki. Da a ce Banu Abbas  basu hau karagar mulki ba da kuwa, ba shakka duk bayanen aikace-aikacensu na sirri da muhimman batutuwan kiransu mai dadi da mara dadi da ya takaita ga zukatansu kadai, ba tare da wani ya san su ba kuma da tarihi bai rubuta komai a kansu ba.

Duk da haka riwayoyin da suke fayyacewa gwargwado kan samuwar mayalwacin kira zuwa ga imamancin Ahlulbaiti (a.s) ba kadan suke ba. Za mu hakura da guda daya mai cewa:-

Wani mutum daga mutanen Kufa ya zo Kurasan, sai ya kira mutane zuwa wilayar Jafar ibn Muhammad (a.s). Wata jama’a sai ta bi shi ta amsa kiransa. wata kuma ta musa masa ta yi inkari wata kuma ta dakata ta yi tsantseni. Sannan riyawar ta ce: Sai mutum daya daga kowace jama’a ya tafo wa Imam Abu Abdillahi (a.s). Mai magana daga cikinsu shi ne wannan da ya dakata ya yi tsantsenin. Sai ya ce : Allah ya kiyaye ka, wani mutum ya zo mana daga mutanen Kufa ya kira mutane zuwa biyayya da wilaya gare ka sai wasu mutane suka amsa masa, wasu suka yi inkari wasu kuma suka ya tsantseni suka dakata. Imam (a.s) ya ce:- “Daga cikin ukun wacce kake ciki? “Ya ce:- Daga jama’ar da ta yi tsantseni ta dakata. Ya ce: To ina tsantsenin ka yake daren kaza da kaza? (sai ya tunatar da shi kasawarsa a wani hali na sha’awa) sai mutumin ya yi shakka. [35]

Kamar yanda ka ji, mai kiran daga mutane Kufa yake, kiran nasa kuwa zuwa imamancin Ja’afar ibn Muhammad Al Sadik (a.s) da wilayarsa da kuma biyayya gare shi ne.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 next