Gudummawar Mace



Matsayin mace na kara haske da tartsatsi mai tsarki a shafukan Alkur'ani ta hanyar surantawarsa ga Muminai maza da Muminai mata a wani sarari na haske, ranar haduwa da Ubangiji, sa'ar cancantar sakamakon da ayyana makomar mutum ta hanyar ayyukansa da tafiyarsa a rayuwa.

Haka muke fahimtar cewa AlKur'ani ya ba managarciyar mace kauna da soyayya, ya kuma yi mata addu'a da gafara, afuwa da rahama; ya kuma kewaye ta da sarari na haske; misalinta ita ce Asiya matar Fir'auna, Maryamu mahaifiyar AlMasihu, Khadija matar Manzon Allah (s.a.w.a.) da Fadimatu 'yar Muhammadu (s.a.w.a.).

Za mu riski girman mace a sakon Musulunci da rayuwar Manzon Allah (s.a.w.a.) ta hanyar da ta daukaka mutuntakarta, ya yabe ta da girmamawa; idan muka san cewa farkon wanda ya yi shahada a Musulunci ita ce Sumayya, mahaifiyar babban Sahabin nan Ammar bin Yasir, jagoran shirka Abu Sufyan ne ya kashe ta. Hakika ta bayar da rayuwarta ga asasan sakon Musulunci, a lokacin da fito-na-fito ya fara tsakanin 'yan ta'adda da dagutai (a wani bangare), da Muahammadu (s.a.w.a.) da wadanda aka raunana da bayi, wadanda suka sami sakon Musulunci mai kwato hakkin dan Adam, mai 'yanto mutane daga jahilci da danniyar mutum ga dan'uwansa mutum (a daya bangaren).

Haka nan da yawa daga matan da aka raunana sun yi gaggawa wajen gaskata Annabi (s.a.w.a.) a farkon kiransa, sun jure cutarwa, azabtarwa da wahalhalu. sun yi hijira zuwa Habasha da zuwa Madina, sun taimaki Allah da ManzonSa (s.a.w.a.) da duk karfin da suke da shi.

Mutuntakar managarciyar mace za ta kara kyautata lokacin da muka shiga sararin nan da ke cike da Shahidai ta hanyar surantawar AIkur'ani da labarinsa da ya bayar da cewa:­

"Kuma kasa ta haskaka da hasken Ubangijinta, aka kuma ajiye takardu (na ayyuka), kuma aka zo da Annabawa da Shahidai, aka yi hukunci a tsakaninsu da gaskiya, alhali su ba za a zalunce su ba". Surar Zumari, 39:69.

Lalle mace Musulma ba ta gano matsayinta na hakika a Musulunci ba tukuna, haka nan namiji Musulmi bai san matsayin mace a Musulunci a bisa hakikanin shi ba tukuna;

don haka ma'aunin mu'amala da alaka suka gurbace, irin wanda ba ya tabbata sai an dawo zuwa ka'idojin Alkur'ani don kowane daga cikinsu ya san hakkinsa da matsayinsa da nauyin da ya hau kansa a kan dayan, da alakarsa da shi.

Macen da ke haniniya a bayan hohon nan na wayewar abin duniya na zahiri wanda babu abin da ke bayansa face mafada da wulakanci ga mace.da ta san abin da ke cikin Musulunci na kima da hakki, da ba ta kira komai ba in ba Musulunci ba. kuma da ta san cewa abin da zai ceto karamarta da hakkinta su ne ka'idojin Alkur'ani.

TANADIN MACE DON CIKA AIKINTA



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 next