Musulmi da Kirista



8- Sakacin Gwamnati

Akwai masu ganin sakacin gwamnati ne ya jawo hakan saboda rashin yi wa tubkar hanci, domin duk sa'adda wani rikici ya faru, to yana bukatar a binciki sababinsa, a kuma yi maganin maimaituwarsa, to amma a wadannan yankunan ba haka ba ne. Maimakon duk sadda ya faru a yi bincike don maganin maimaituwa, da kuma yi wa masu laifi ukubar sakamakon abin da suka yi, sai maganar ta sha ruwa kawai.

Wannan lamarin yana daga cikin abubuwan da kowa ya yarda yana daga cikin abin da yake sake haifar da rikici, kuma matukar ba za a yi wa tubkar hanci ba, zai ci gaba har abada.

Abin takaici a nan shi ne; da gwamnan zai yi rashin lafiya da yanzu ka ga ya yi tafiya har kasashen waje domin kawai ya ga likitan da zai duba ya gano musabbin ciwon da yake damunsa don yi masa maganinsa, amma irin wannan mutumin ne babu ruwansa da al'ummar da aka kashe a jaharsa, bai damu da gano ciwon da yake damun al'ummarsa ba! Domin yana da tabbacin abin ba zai shafe shi ba, ba kuma zai shafi matarsa da 'ya'yansa ba!.

Kuma idan ya tabbata cewa akwai hannunsa ma, to wannan lamarin shi ne ya fi kowanne muni!.

 

9- Kyashi da Hassada

Akwai masu jingina irin wadannan rigingimu da ganin cewa kyamar juna da kyashi, da hassada ce take jawo shi! Idan haka ne kuwa to akwai abin bakin ciki a kasa kamar Nijeriya da kowane dan kasa yana da ikon ya zauna inda yake so don samun ci gabansa da na al'ummar kasarsa, amma a samu wasu suna yi wa wasu hassadar ci gaban da suke samu.

Ci gaban mutum daya na kasa baki daya ne, domin misali wanda ya yi odar motoci ya sayar to babu wanda zai amfana sai 'yan kasa, haka nan sauran abubuwan more rayuwa da amfanin al'umma. Amma sai ciwon hassada da kyashi ya shiga al'umma daya, ana yi wa juna hassada da keta da mugunta, wannan lamarin ne ya sanya da rikici ya tashi babu wani abu da wasu suke kai hari kansa sai kayan kasuwancin al'ummar nan.

Idan dai wannan lamarin ya kasance yana daga cikin dalilai to shi ma yana bukatar aiki tukuru domin wayar da kan wannan al'ummar, kuma nauyi ne da ya hau kan malamai da sauran masana da gwamnati kai tsaye. Sai dai yana da nauyi sosai kan malaman addinai don su wayar da kawukan mabiyan addinai kan munin lalacewa halaye, da mummunan sakamakonsa wurin Allah!.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next