Musulmi da Kirista



Don haka ne duk sa'adda wannan lamarin ya faru to yana bukatar sanya hankali, kuma babu wanda ya kamata ya zama hakan sai masu jagorancin al'umma, sai dai mutane Jos ba su yi sa'ar jagorori ba, domin tunanin masu tafiyar da mulkin yankin bai dace da yanayin 'yan adamtaka ba. Sai duniya ta kasance tana da hasashe mai ban mamaki, sai zato ya zama yakini, sai kokwanto ya zama gaskiya. Idan da an sanya hankali zamu iya lura da wasu abubuwa kamar haka:

Ba yadda za a yi musulmi ko kirista da yake yankin Jos ya sanya wannan bom domin bom din ya kashe duka musulmi da kiristan Jos ne.

Musulmai suna girmama bukin da ya shafi annabi Isa (a.s) don haka ba yadda za a yi ranar da ake murnar haihuwarsa su sanya bom don lalata bukin.

Talaka musulmi da kirisata da suke wannan yankin ba yadda za a yi su sanya wannan bom din domin babu mamaki ba su taba ganin bom ba, kai yawancinsu ba su ma taba rike bindiga ba, ba su san yadda ake harba ta ba!.

Ko bindiga ce aka samu a hannun wasu mutane, to laifin hukuma ne balle kuma bom, don haka tun da alhakin tsaro nata ne, laifin yana koma wa kanta, don haka ne dole ta bayar da tsaro ga dukkan al'ummarta babu bambancin addini ko kabila!.

Idan wani abu irin wannan ya faru dole ne a bari gwamnati mai hankali ta yi bincike ta yi iya kokarinta don gano musabbabin abin, zai iya yiwuwa bisa hatsari ne ya fashe, kamar a ce yana hannun soja ne da ya zo wucewa da shi don kai shi wani wuri bisa umarnin gwamnati, ko kuma wasu 'yan ta'adda ne suka dasa shi, kuma su waye? Kuma mene ne hadafinsu? da sauran bincike!.

Mu musulmi idan ya tabbata akwai wani musulmi da yake da hannu kan sanya Bom a Jos to mu ne farkon masu goyon bayan a tsayar masa da dukkan hukuncin da ya dace, domin idan ya yi da sunan kansa ne, to ya yi ta'addanci, amma idan ya yi da sunan addininsa ne, to laifinsa ya yi girman da ba zamu taba yafe masa ba, kuma muna neman a zartar masa da hukunci mai tsanani kan cin mutuncin addininmu da ya yi!.

Sanya Bom a kasashen gabas ta tsakiya ya sanya neman bata musulunci da sunan cewa addinin ta'addanci ne, wannan kuwa shi ne babban rashin adalci da ake yi wa musulunci, domin kafin masu sanya Bom su kashe wanda ba musulmi ba daya, sun kashe musulmi dubu. Don haka wadanda suke sanya wannan Bom ko da kuwa sun kira kansu musulmi to ba musulmai ba ne, sai dai su makiya musulunci da musulmai ne!.

 

7- Kasashen Waje



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next