Musulmi da Kirista



Rashin adalcin gwamnatin jahar Fulato kan 'yan wannan jahar yana daga cikin abin da ya fi yawo a bakunan mutane, kuma wannan ne yake jawo rikici a wata mahangar. Domin wadanda suka yi laifi suka kashe mutane ba a taba su, wadanda kuwa aka zalunce su idan suka rama sai a gaggauta kama su, misalai da yawa ne suka faru kamar na kama Fulani da aka yi a bayan rikicin January 2010, bayan an kashe musulmi an kona su, an kashe Fulani an kama shanunsu babu ko mutum daya da gwamnatin Jaha ta kama, amma suna zuwa su dauki fansar shanunsu da aka kashe cikin lokaci kankani sai ga shi duk an kama su a hannun 'yan sanda!.

Don haka wannan wuta ce wacce zata yi ta ruruwa a ko da yaushe, babu wani lokaci har abada da zata tsaya matukar bakin zalunci ya yi katutu a wannan nahiya tamu kuma babu wani adalci da wanda aka zalunta yake gani. Wannan lamarin yana nufin wata rana ya tsallaka jahohin Jos, da Bauchi ya watsu duk kasar Nijeriya, a nan ne wanda yake jin dadin wannan lamarin zai gane cewa kasarsa zata yi masa wahalar zama saboda zaluncin da ya yi wa al'ummarsa.

 

14- Zafin Addini

Wannan ra'ayin yana ganin rikicin na addini ne kawai ba wani abu ba, kuma wasu addinan ne suke kyamar wasu, don haka suke ganin kawar da su da neman ganin bayansu. Don haka ne ba za a samu kwanciyar hankali ba matukar kiristan wannan wurin yana ganin musulunci matsala ce gare shi kuma zai ci gaba da kai masa hari duk sadda ya samu dama!.

Suna ganin wannan lamarin ne ya sanya kiristan wurin yake kiran musulmi bako, don haka duk musulmai baki ne, kuma dole ne su bar wannan yankunan baki daya. Sai dai wannan dalilin ya fi kama da na kabilanci, ko 'yan garanci, ko bangaranci, amma ana iya jingina shi da addini saboda shi mai kin abu yana iya ba shi duk sunan da ya ga dama don bata shi.

Idan kuwa ya tabbata cewa kin wani addini mai girma kamar musulunci ne ya jawo wannan to yana bukatar sanin masu wannan tunanin, shin duk kiristan wannan wurin ne, ko kuwa wasu daga cikinsu ne, ko wata Coci ce mai wannan tunanin. Duk wadannan abubuwan suna iya sanya bincike mai ma'ana da zai iya gano asalin matsalar, idan kuwa ba haka ba, to wannan yana nufin ci gaban wannan matsalar ko da yaushe, kuma a ko'ina!.

Idan duk wadannan abubuwan suka tabbata to duk kowa ya yi tarayya cikin rikicin da fitina, don haka sai a zauna domin ganin an warware matsalar daga tushe.

 

15- Ramuwar Gayya



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next