Musulmi da Kirista



3- Makircin Siyasa

Akwai magana mai karfi da take yawo a cikin wannan al'ummar cewa masu wannan rikici da masu tayar da shi suna samun karfafa daga 'yan siyasa ne, kuma su 'yan siyasar suna da hadafi na musamman kan wannan lamarin wanda yake shi ne tabbata kan mulki, don haka sai su rika tayar da wannan rikici domin kashe mutanen da suke ganin abokan hamayya ne da zasu iya cin nasara kan su.

Wannan ra'ayi ne mai karfi matukar gaske, domin 'yan kabilar gwamna da mutanensa ko masu addini daya da shi suna iya yin kwanaki suna kisa amma babu jami'an tsaro a kan titina. Wani abin takaici da za a karar da dukkan musulmin da suke wannan nahiya to gwamnatin Jaha ba zata iya tura ko da dan sanda daya ba domin ba su kariya har sai dai gwamnatin tarayya ta sanya hannu, don haka ne wannan ra'ayin yake da karfi matukar gaske.

Inda wannan ra'ayi yake dada karfi bayan abin da muka kawo shi ne abin da wadanda suke wannan wuri suke gani da idanuwansu, da abin da jaridu suke bugawa, da kiraye-kirayen da ake yi wa gwamnatin tarayya na ta shiga cikin lamarin domin bayar da kariya duk suna nuna hakan.

Idan da za a ce duk wani gwamnan da aka samu a jaharsa an yi irin wannan rikicin ko da kuwa mutum daya ne aka kashe, to shi ba kawai ya rasa mulkinsa ba ne, wannan yana iya kai shi ko ga rasa nasa ran, ko kuma zaman gidan yari har mutuwa, da ba zaka taba samun wannan ya faru a ko'ina ba cikin fadin kasarmu.

Idan akwai wasu dokoki masu tsauri kan mai mulki, to da zarar gwamna ya ji wuta ta huru daidai da minti daya ba zai yi sakaci ba wurin kare rayukan wadanda aka zalunta. Kuma da ka gan shi ya gaggauta tsayar da adalci kan wadanda suka yi wannan lamarin domin babu hannunsa, kuma da zai yi wa masu yin wannan harin hukuncin da wani ba zai sake sha'awar kawo irin wannan rudun ba!

 

4- Ingizawar Coci

Akwai masu ganin Coci ce take tunzura kirista da ingiza su don auka wa musulmi da kisa, sai wannan lamarin ya kasance ya yi kamari kuma ba yadda za a yi ya dakata tun da ya samo daga akida ne, don haka dole ne a dakatar da abin daga Coci domin a samu zaman lafiya.

Sai dai wannan lamari ne wanda ban samu wani dalili kansa ba, domin idan Coci tana yin haka, sai dai idan Cocin Jos ce take yin haka, ko kuma wasu daga malaman Cocin Jos, domin akwai Coci a ko'ina a Nijeriya amma ba a samu wannan lamarin ba. Kuma tun da akwai Coci amma ba a samu tana yin haka ba, sai dai idan masu wannan tunani su ce daga baya ne ta fara yin wannan da'awar kawar da musulmi da sunan "Baki" daga garin Jos! To wannan ma yana bukatar dalili daga masu wannan ra'ayin.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next