Musulmi da Kirista



Hurrul amuli ya ambaci cewa: Imam Ali (s) yana tafiya a cikin lungunan garin Kufa wata rana, sai ya ga wani mutum yana rokon mutane (yana bara), sai ya yi mamaki sosai, sai ya juya da shi da wadanda suke tare da shi suna tambayarsa mene ne haka?

Sai ya ce: Ni tsoho ne kuma kirista na tsufa ba na iya aiki kuma ba ni da wata dukiya da zan rayu da ita, sai na shiga bara.

Sai Imam Ali (s) ya yi fushi ya ce: Kun sanya shi aiki yana saurayi sai da ya tsufa zaku bar shi?! Sai ya yi umarni a sanya wa wannan kirista wani abu na albashi daga Baitul-mali da zai rika rayuwa da shi[2].

Haka nan ne musulunci ya yi mu'amala kyakkyawa ga kowane mutum ba tare da la'akari da addininsa ko launinsa ko kabilarsa ba!. Don haka a yaushe ne aka samu sabanin hakan a rayuwar musulunci! Tabbas idan wani abu sabanin haka ya wakana to sai dai idan an kauce wa koyarwar musuluncin ce.

Sannan kiristanci ma ya zo da salon kira da kyautata halaye da tausayi da jin kai kamar dai yadda musulunci ya zo da shi, sai dai musulunci ya zo da kari kan hakan da abubuwa masu yawa domin shi tsari ne da yake da mahanga a kowane fage na ilimi da aiki.

Al'ummarmu ta dade tana zaman lafiya a tare tsakanin musulmi da kiristoci, amma sai ga shi a wadannan shekarun na karshe abin ya yi kamari, ta yadda aka samu kashe-kashe baji-bagani tsakanin masu wadannan addinai. Ya isa kawai wancan ya ga wannan sai ya hau shi da kisa da duka! da kona dukiyarsa! da rusa gidansa!. Wannan abin takaici yana wakana lokaci bayan lokaci, amma sai ya yi ta maimaituwa ta fuska iri daya, kuma a wuri daya, a kasa daya, amma babu wani mataki na hankali ko doka da masu hukunci a wannan kasa suke dauka. Imma dai saboda mai hukuncin yana ganin zai hukunta masu addini daya da shi, ko kuma zai hukunta masu yare daya da shi, ko kuma shi ma yana goyon bayan irin wannan abin a boye.

Sai ra'ayoyi suka bambanta kan sababin wannan mummunan lamarin; da mai ganin jahilci ne, da mai ganin siyasa ce, da mai ganin talauci ne da ya yi wa al'umma yawa, da mai ganin coci ce take tunzura kirista auka wa musulmi, da mai ganin akida ce karkatacciya da take kunshe cikin tarihi mai ramuwar gayya na abin da aka yi wa wadanda ba musulmi ba, da mai ganin tuhumar musulmi ce da kirista suka yi kan bom da aka sanya, da mai ganin akwai hannun kasashen waje kan wannan lamari, da mai ganin sakacin gwamnati ne ya jawo hakan saboda rashin yi wa tubkar hanci, da mai ganin cewa kyamar juna da kyashi, da hassada ce ta jawo wannan lamarin. Muna iya nuni da wasu ra'ayoyi a takaice da ake muhawarori kansu kamar haka:

 

1- Bakin Talauci

Talauci mummunan abu ne a cikin al'umma, don haka ne musulunci ya yi kokarin ganin matakin farko shi ne kawar da shi, sai ya sanya dokokin humusi, da zakka, da sadaka (cibiyoyin ayyukan alheri a yau da jin kan raunanan mutane), da kyauta, da lamunin rayuwa, da biyan bashin talaka, da aurar da shi, da ba shi jari don sana'a, kuma ya kara da halatta wa mutane raya wuri da cewa; idan suka raya wuri to na wanda ya raya shi ne.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next