Musulmi da Kirista



 

10- Rashin Mu'amala

Wasu kuwa suna ganin rashin mu'amala kyakkyawa daga musulmi da kyama da suke nuna wa kiristoci ne ya jawo hakan, don haka sai wadannan kiristocin suke ganin kamar ana yi musu wani ganin raini da wulakanci, ta yadda hatta da sunan da ake gaya musu kamar kalmar arne tana yi musu ciwo, don haka sai wannan ya yi musu zafi, sai suka fara tunanin yadda zasu kawo karshen wannan lamarin, sai su ma suka fara gaya wa musulmi wannan sunan na arna ko kafirai, sannan wannan bai isa ba, sai suka fara tanadin ganin bayan dukkan musulmi da kashe su, da lalata dukiyarsu.

Idan wannan lamarin ya tabbata to an samu sakaci da takaitawa daga bangarori biyu ke nan; bangaren musulmi da na kiristoci, sai dai hanyar da kirista suka dauka don rama laifin wancan sunan da ake gaya musu ta saba wa hankali da tunani mai kyau. Domin kamar yadda muka kawo ne cewa kowane laifi a bisa doka ta hankali yana da nasa mataki gwargwadon girmansa ne, babu zalunci babu karbar zalunci.

Matakin da ya dace a nan bai kamata ya kai ga kisa ko halaka dukiyar al'umma ba, mataki ne da ya kamata kotu da malamai su warware shi, sai a yi dokar da ta dace da shi!. Ta yadda babu wani musulmi da zai sake gaya wa wani kirista sunan arne, sai ya gaya masa sunansa da hatta da musulunci abin da ya san shi da shi ke nan.

Kai hatta da kalmar kafiri bai kamata a gaya wa kirista ba matukar tana da ma'anar wanda ba shi da addini ne. Kalmar kafiri kalma ce mai fadi da tana da ma'anoni daban-daban, don haka a yankunanmu tana da ma'ana da su masu addinai da ya saba wa musulunci ba sa fahimtarta, don haka sai a kira su da sunan da shi ne sunansu na yanka da musulunci ya kira su da shi, kuma suka kira kansu da shi.

Ayar Kur'ani a surar Hajji: 17, ta nuna mushrikai daban, kirista daban, domin sunansa ke nan hatta a musulunci. Kalmar kafiri tana da fadi, wani lokaci hatta da rashin godiya da butulci an kira shi da kafirci, wasu mazhabobi kamar wahabiyawa suna kiran wasu musulmin kafirai saboda suna yin wani aiki da ya saba wa musulunci a mahangarsu, don haka kalmar kafirci sifa ce ba suna ba ce, sifa ce da tana iya hawa kan wanda yake kiran kansa musulunci idan ya kauce wa hanya ta gari, kamar musulmin da suka yi imani a fili amma bai kai zuci ba (munafukai) an kira su da kafirai a littafin Allah, haka ma wanda ya yi imani da wani bangare, bai yarda da wani ba, an kira shi da kafiri.

Don haka matukar matsalar suna ce to ya hau kan masana su tashi domin ganin sun wayar da kan musulmi kan mene ne musulunci. Sai dai hanzari ba gudu ba, duk sa'adda na yi tunani irin wannan na kan samu cewa, sama da kashi 97% na masu kiran kansu malaman musulunci a kasashenmu ba su ma gama sani ma'anonin da musulunci yake amfani da su shi kansa balle kuma su wayar da kan sauran musulmi.

Wallahi da musulmi sun san musulunci kamar yadda yake, sun san iliminsa kamar yadda yake, sun bi kofar birnin ilimi annabin rahama (s.a.w) imam Ali dan Abudalib (a.s) da ba a samu wani mutum daya da yake kyamar musulunci ba, da dukkan duniya sun rungumi wannan rahama da ta bayyana ta hannun annabin Allah na karshe Muhammad al-mustafa (s.a.w).

 



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next