Musulmi da Kirista



Wannan ma ya shafi lamarin rikicin da ya faru kwanan ne wanda sakamako fashewar bom ya jawo shi. Masu wannan ra'ayin suna danganta abin da wasu kasashen waje da suka saba haifar da rikici tsakanin al'ummu don cimma burinsu, suna bayar da misalin irin wannan da yake faruwa a kasashen gabas ta tsakiya.

Irin wannan Fashewar Bom yana faruwa a wasu kasahe, kuma yana kai wa ga rikici kamar yadda zamu kawo a misali, irinsa ya faru a Labnon da ya kashe tsohon shugaban kasar Rafik Hariri. Sau da yawa irin wannan idan ta faru ana zargin juna ne tsakanin jama'u masu rigima da gaba, wani lokaci kuma a zargi kasashen waje.

Muna iya ganin lokacin da ya faru sai nan take aka zargi Syria da cewa ita ce, har ma aka sanya shedun karya domin su bayar da shedar zur, sai dai duk da an gano shedun karya aka sanya amma sai aka takura kasar Syria da fita daga Labanon.

Daga nan ne sai Syria ta dora alhakin sanya bom din kan mutanen da suke gaba da ita a cikin Labanon masu taimako daga kasahen larabawa da turai, da Isra'ila a matsayin kasar da take gaba da ita da cewa su suka sanya Bom din don su yi kamfen din korarta da shi daga Labanon.

Da yake dan Adam bai san gaibi ba, kuma yana jahiltar abubuwa masu yawa, kuma yana da sauki a wannan yanayin farfaganda a yi wasa da tunaninsa, sai kuma aka koma ana Zargin Lahud tsohon shugaban kasar Labanon bai ji ba, bai gani ba.

Da wannan bai samu ba, sai kuma aka koma yin sabon Fayel din zargi wanda yake neman ya dora alhakin abin a kan kungiyar Hizbullah ta Labanon, kuma aka so yin amfani da wannan domin rusa ta saboda hadafin babban makiyinta kasar Isra'ila ya tabbata na ganin bayanta.

Wannan lamarin ne ya sanya ita kuwa Hizbullahi ta kawo cikakkun shedu da nuna cewa tana da wasu karihar shedun idan ana neman karin hujjoji kan cewa Isra'ila ta sanya bom din ta kashe shi domin ta samu hargitsa kasar sai ta shigo kamar yadda ya faru a shekarun baya don dai ta shigo wannan karon ta rusa Hizbullah.

Wani abin da yake bayar da mamaki shi ne, shi Firaministan da aka kashe yana da kyakkyawar alaka da kungiyar ta Hizbullah, wannan lamarin ne yake sake ba wa masana siyasa hujja da nuna cewa lallai ba ta da hannu a kashe shi, domin masoyinta ne.

Da wannan ne Hizbullah da wasu kungiyoyi na kasar suka kai ga natijar cewa Isra'il ce ta sanya Bom don ta kashe shi, sai kuma ta hargitsa kasar ta cikin gida. Kuma suna dada karfafa wannan da cewa; bayan wannan lamarin ba wanda aka jefa sai masu gaba da Isra'il, wanda suka hada da Syria da Hizbullah domin fitar da Syria daga kasar, ita kuwa Hizbullah a kawar da makamanta, wannan ne kawai kuma matakan da zasu kawar da barazanar da take damun Isra'il da ta hana ta shiga Labanon don mamaya kamar yadda ta so.

 



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next