Hadisan Annabi



DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI

Yana daga cikin abinda mazahabin Ahlul Baiti (A.S) ya kebanta da shi girmama hadisan Wasiyyan Manzo Bayan hadisan Manzon (S.A.W) domin hadisansu sun kasance daga hadisansa ne, wato kamar yadda hadisansa suke fassara Alkur’ani haka ma hadisansu da umarnin Manzo (S.A.W) na a yi riko da su da kuma Alkur’ani bayansa (S.A.W) . Sa’annan falaloli da dama sun zo akan hardace hadisai arba’in don haka wadannan hadisai arba’in da ‘yan kai mun tanade su muka zuba su a nan domin neman albarkar wancan hadisi da kuma fatan a hardace su a kiyaye su a kuma yi aiki da su.

قال رسول الله صلّى الله عليه Ùˆ آله : Ù…ÙŽÙ† أصلَحَ فيما بَينَهُ وبَينَ اللهِ أصلَحَ اللهُ فيما بَينَهُ وبَينَ النّاسِ.

Manzon Allah (S.A.W) ya ce :

Duka wanda ya gyara tsakaninsa da Allah to Allah zai gyara masa tsakaninsa da mutane.

قال رسول الله صلّى الله عليه Ùˆ آله:   Ø®ÙŽÙÙ اللهَ كَأَنَّكَ تَراهُ فَإِن كُنتَ لاتَراهُ فَإِنَّهُ يَراكَ .   

Manzon Allah (S.A.W) ya ce :

Ka ji tsoron Allah kamar kana ganinsa idan ka kasance ba ka ganinsa ai shi yana ganinka.

قال فاطمه زهراعليها السّلام: Ù…ÙŽÙ† أصعَدَ إلَى اللهِ خالِصَ عِبادَتِه ِأهبَطَ اللهُ إلَيهِ أفضَلَ مَصلَحَتِه  

FatimatuzZahra (AS) tana cewa:

Duk wanda ya kusanta da Allah yana mai tsarkake ibadarsa Allah zai saukar masa da mafificiyar maslaharsa (ya biya masa mafificiyar bukatarsa)



1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next