Mutum Mai Kamala



1.     Daukewar fari da ya same su da su da mutanensu

2.     Aminci a cikin al’ummarsu gaba daya

3.     Yalwar arziki da hayayyafar dabbobinsu

Babarsa ta rasu yana dan shekara shida, sannan sai kakansa Abdul mudallabi ya cigaba da renonsa, shi ma ya rasu yana dan shekara takwas, wanda a sakamakon haka ne baffansa Abu Talib (A.S) da kuma matarsa Fatimatu ‘Yar Asad (A.S) suka dauki nauyin renonsa.


Kasuwancinsa

Kasancewar gidan Abu Talib yana da karancin yalwa wannan ne ya sanya manzo (S.A.W) ya motsa domin ganin ya dauki nauyin wannan gida, ta hanyar karbar kwadagon kasuwanci na fatauci kamar yadda yake al’amari sananne a wannan zamani.

Manzo ya yi fatauci da dukiyar Khadiza (A.S) da shawarar Abu Talib (A.S), kuma wannan ya samu alheri da yawa da albarka da ba ta lissafuwa.

Sai ya yi fatauci zuwa Sham da dukiyarta ya dawo yana mai cike da hannu mai albarka da kuma amana da ba ta taba gani ba. Musamman daga labaru da ta samu daga mutane daban-daban kamar bawanta Maisara.

Annabi mai girma ya bayar da dukkan ribar da ya samu na hakkinsa na fatauci ga amminsa Abu Talib gaba daya domin yalwatawa ga iyalansa, wannan al’amari ya sanya shi farin ciki mai yawa da abin da dan dan’uwansa Muhammad (S.A.W) ya yi masa na kyauta[5].


Aurensa

Manzon Allah (S.A.W) ya auri mace mafi kamala a cikin larabawa da mafi yawa daga manyan Makka sun so aurenta amma ta ki amincewa da su saboda kamalarta da kuma yanayinsu na ba tsararrakinta ba ne su a halaye.

Musamman ma wasu suna sonta ne domin wani abu na duniya da take da shi kamar kyawunta ko dukiyarta, wasu kuma ma’abota dukiya maras misali ne amma duk da haka taki amincewa, sai ta yarda da neman da Abu Talib (A.S) ya yi daga gareta na aure da dan dan’uwansa Muhammad, kuma ta amsa masa abin da ya nema, domin kamalarsa da kuma darajar gidansu a cikin larabawa da kuma kamewar Manzo (S.A.W) da rikon amanarsa.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 next