Mutum Mai Kamala



·        Khandak

·        Banu Kuraiza

·        Banu Kainuka’a

·        Khaibar

·        Fathu Makka

·        Hunain

·        Da’ifa


Hajjin Bankwana

A cikin shekara ta goma da yin hijira ne Manzo (S.A.W) ya yi hajji domin ya sauke wajibi kuma ya sanar da al’umma ayyukan hajjinsu, kuma ya tafi tare da dukkan matansa da ‘yarsa Zahara (A.S), kuma kabilun larabawa mabanbanta da suka hada musulmi sama da dubu dari 100 000 ne suka yi hajji tare da shi.

Imam Ali (A.S) ya zo daga Yaman domin ya riski Manzon Allah a Makka, sai Manzo ya yi farin ciki da zuwansa da kuma irin nasarar da ya samu a Yaman, sannan Manzo ya ci gaba da ayyukan hajji wanda daga karshensa ya yi huduba ga musulmi kuma ya yi bankwana da su, ya ayyana musu wasiyyinsa kuma halifansa bayansa, kuma ya sanar da su da yawa daga hukunce-hukuncen addini.

Hudubar Hajjin Bankwana

 Abin da nake son kawowa a nan shi ne abin da hudubar hajjin bankwana ta kunsa domin mu ga ilimi da hikima da kuma sakon Manzon rahama zuwa ga al’umma gaba daya a dunkule, sannan mu auna kawukanmu mu ga ni idan mun bi wasiyyar Manzon rahama (S.A.W) da ta kunshi wadannan abubuwan:



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 next