Boyayyar Taska



Bayan halakar da mutanen da Dufana da kuma wafatin Annabi Nuhu (A.S) sai Ashararai daga zuriyarsa Hamu da Yafusu da sahabbansa suka yi galaba a kan Wasiyyinsa Samu (A.S) da Shi’arsa suka kafirce wa Allah da Manzonsa Nuhu (A.S), suka kuma dawo da bautar gumaka da sunansu na da Ya’uka, da Yagus, da Nasra, da Suwa’a, da Wudda. Sarauta ta ci gaba a hannun zuriyar Kabila da I’waja har zuwa kan Kan’ana baban Namarzu kafirin sarkin nan a lokacin Annabi Ibrahim (A.S) wanda ya kasance daga zuriyar Hamu Dan Nuhu ne. Amma Samu Dan Nuhu (A.S) ya ci gaba da rike sakon Allah, kuma sakon bai gushe ba daga wasiyyi zuwa wasiyyi mai bi masa har zuwa kan Nakhur kakan Annabi Ibrahim (A.S) zuwa Tarikha babansa, har zuwa kansa (A.S).

Bayan Annabi Ibrahim Da Musa (A.S)

Amma idan ka ji abin da ya faru bayan wafatin Annabi Ibrahim (A.S) sai ka zubar da hawaye, domin annabawa da salihai daga zuriyar Ibrahim (A.S) ba su samu damar yin hukunci ba sai na dan lokaci kankani, ashararan ‘ya’yan Ishaka (A.S) suka samu galaba a kan annabawa da salihai suka karkashe su, suka kuma kora wasunsu zuwa dazuka da tsaunuka haka nan a bin ya ci gaba har zuwan Annabi Musa (A.S). Duba Tarihin Isu Dan Annabi Ishak da galabar da ya samu kan Annabi Ya’akub (A.S) wasiyyin Ishak (A.S), Isu ya ci galaba kan Annabi Ya’akub (A.S) ya kuma kwace tafiyar al’amarin Baitul Mukaddas daga hannun Annabi Ya’akub (A.S), an ce Isu ne farkon wanda ya kirkiro kebance hurumi ga mai mulki kuma farkon wanda ya kirkiro haraji. Amma annabi Ya’akub (A.S) ya ci gaba da hakuri babu iko a hannunsa ya kuma yi wasiyya ga Annabi Yusuf (A.S), mai karatu ba na tsammanin zaka iya mantawa da kissar Annabi Yusuf (A.S) da wahalar da ya sha a hannun munafukan ‘yan’uwansa. Haka nan al’amari ya ci gaba har zuwa kan Annabi Musa (A.S).

Labarin wahalhalun da Annabi Musa (A.S) ya sha a hannun Bani Isra’ila ba boyayye ba ne ga wannan al’umma da aka saukar wa Kur’ani mai girma, shi ma ya kasance yana da Wasiyyai biyu da dayansu shi ne Annabi Haruna (A.S) wanda ya rasu a lokacin rayuwar Annabi Musa (A.S) wanda ya tafi ya bar shi da al’umma cikin kwana arba’in kawai, amma a cikin wadannan kwanaki sai aka yi wa wasiyyin tawaye aka ma dauki Musa Samiri wanda yake munafiki ne a al’ummar Annabi Musa (A.S) kuma Annabi Musa (A.S) ya kore shi daga rundunarsa, amma ya dawo ya yi sihiri ya kuma iya jawo hankulan ‘Ya’yan Isra’ila suka bar Annabi Haruna (A.S) suka bi Musa Samiri, a nan muna iya tambayarka mai karatu? yaya kake gani idan da ya zamanto Musa ya rasu ne fa? kuma yaya al’amarin zai kasance da ba zai dawo ba.

To haka nan kuwa abin ya faru, sai ga shi kafin rasuwarsa ya shelanta wa al’ummarsa wasiyyinsa Yusha’u Dan Nun (A.S) amma bayansa sai al’ummar ta ki bin Wasiyyin ta hada kai da munafukai aka wahalar da shi aka kuma yi masa tawaye. Yahudawa ba su bi Yusha’u Dan Nun (A.S) ba sai ‘yan kadan shi ma a lokacin suna cikin dimuwa ta shekara arba’in ne da Allah ya saukar musu saboda kin biyayya ga Annabin Allah Musa (A.S). A wannan shekarun dimuwar ne Allah ya dauki ran Annabawansa; Annabi Musa (A.S) da wasiyyinsa na farko Annabi Haruna (A.S) zuwa gare shi, amma bayan shekara arba’in dimuwa ta kau sai Annabi Yusha’u (A.S) ya gaya musu sakon Allah na su ta shi su yaki mutane Jabberai. Amma suka yi masa tawaye aka nemi kashe shi, sannan aka hada runduna ta munafukai domin yakar sa, wani abin mamaki shi ne rundanar da ta yake shi ta kasance karkashin jagorancin matar Annabi Musa (A.S) Safura ‘yar Shu’aibu (Amma wasu ma’abota tarihi sun nuna ba ‘yar Annabi Shu’aibun da ya aura a garin Madyana ba ce domin ita sunanta Safra).

Da haka ne fajirai da munafukai suka yi galaba a kan muminai, rigingimu suka ci gaba har ta kai ga kashe Annabi Yusha’u (A.S) da kashe sauran wasiyyan Annabi Musa daya bayan daya. Aka assasa Daular Alkalai (kamar yadda ake kiranta) kabilun Bani Isra’ila suna shugabanci irin na kama ka ba ni bisa zagaye na dangi-dangi, zamani ya ja har zuwa lokacin Annabi Dawud (A.S).

Wasiyyan Dawuda Da Sulaiman (A.S)

Amma bayan wafatin Annabi Sulaiman (A.S) Tarihi ya fadi yadda Sahabbansa da ashararan danginsa suka yi wa wasiyyinsa Asifu Dan Barhaya (A.S) da jama’arsa, suka kawar da shi daga rike shugabancin da Annabi Sulaiman ya bar shi a kai. Da tun farko sun san cewa Annabi Sulaiman ya rasu da ba su bari Asifu (A.S) ya rike mulki ba koda da rana daya, da mulkin bai kai shekara a hannunsa ba. Haka nan aka kawar da shi aka dawo da Rahab’am makiyin Annabi Sulaiman wanda Annabi Sulaiman (A.S) ya kore shi zuwa kasar Misira ya kuma haramta masa dawowa Falasdin, aka dora shi kan mulkin Annabi Sulaiman (A.S) sannan daga baya suka yi ta sabani, aka lalata falsafa[4] da koyarwa ta Annabi Sulaiman aka kirkiro hadisai na karya har ma da na shirka aka jingina ga Annabi Sulaiman (A.S) har Allah ya tsarkake shi a cikin Kur’ani mai girma. Haka nan Daular ta daddare ta rarraba tsakaninsu saboda yawan sabani da son juciya da jahilci, mafi yawancinta ya fada hannun makiyansu, yankin Kudus ya rage a hannunsu, aka dauko daya daga zuriyar Annabi Sulaiman wanda yake ba wasiyyi ba ne nasa aka ba shi gwamnan garin Al-khalil, amma makiyan Annabi Sulaiman da ya kore su a rayuwarsa mulki ya rage a hannunsu ne.

Bayan Masihu Mai Albarka Isa Dan Maryam

Amma bayan Isa (A.S) ya daukaka zuwa ubangijinsa sai ga ukuba mafi tsanani daga al’ummarsa da Rumawa a kan wasiyyansa. Rumawa ba su gushe ba suna korar wasiyyansa musamman Sham’unus Safa da sauran Hawariyawa da muminai da suke tare da su, har lokacin da Bulus ya zo bayan shekara talatin da daukaka Annabi Isa (A.S) ya yi da’awar cewa ya ga Isa (A.S) ya kuma bayyana gare shi a hanyarsa zuwa “Sham” daga sama a garin “Hauran”. Bulus ya kasance mutum ne da yake kashe duk wanda yake bin da’awar Annabi Isa (A.S) kuma bai san komai game da addinin Isa (A.S) ba, ya kasance yana bin su gari gari yana kashewa, amma sai rana daya ya zo ya yi da’awar Isa (A.S) ya bayyana a gare shi yana mai cewa da shi: “Don me ya sa zaka rika gaba da ni haka”.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 next