Boyayyar Taska



Kammala wannan littafin ya zo daidai da ranar haihuwar Sibdul Akbar Imam Hasan Dan Ali Dan Abi Dalib (A.S) 15 Ramadan watan azumi 1424 Hijira kamariyya, daidai 19 Aban 1382 Hijira Shamsiyya. Wanda ya yi daidai da 10 Nuwamba 2003 Miladiyya, Ranar litinin a kidayar nan kasar Farisa. Don haka ne nake fatan Allah (S.W.T) ya karbi wannan aikin, ya sanya yardarsa a ciki, ya sanya mu cikin wadanda ake gafartawa zunubai a wannan wata mai albarka, kuma ya mika ladan ga Imam Hasan (A.S).

Hafiz Muhammad Kano Nigeria

hfazah@yahoo.com

Wasiyyan Annabawa

Dabi’ar Mutum

Wani abin mamaki, al’ummu[3] da dama sun gabata, amma a kullum abin da yake faruwa a cikin al’ummar da ta gabata idan ta baya ta zo sai ta maimaita irinsa. Wannan wani abu ne da ayoyin Kur’ani mai girma da Hadisai madaukaka suka yi nuni da shi a fadinsa Ubangiji madaukaki yana cewa:

“Shin sun yi (wa juna) wasici da shi ne? Wato shin wadanda suka gabata suna Wasiyya ga masu zuwa ne idan kun zo ku ma ku yi irin abin da muka yi? Wannan al’umma tamu ba ta kubuta daga irin wannan tarko ba domin ta fuskanci irin abin da al’ummar Annabi Musa (A.S) da Isa (A.S) da Annabawan da suka gabace su (A.S) suka fuskanta kuma ta bi sawunsu taku da taku, don haka sai muka ga bari mu kawo Tarihi takaitacce na Ma’asumai kuma Wasiyyan Annabawa da suka gabata kamar yadda ya zo a littattafan Tarihi. Amma bari mu fara da uwa uba Annabi Adam (A.S) wanda yake babanmu kuma daya daga cikin bayi da Allah bai yi kamarsu ba a cikin halittunsa.

Wasiyyan Annabi Adam (A.S)

Tarihi ya tabbatar mana da cewa, Annabi Adam (A.S) yana da wasiyyai guda biyu; daya an kashe shi a lokacin rayuwar Annabi Adam (A.S) wato shi ne Habila (A.S) da kabila la’ananne ya kashe shi, wannan al’amari ya faru ne yayin da Kabila da Habila suka yi kurbani sai Allah ya karbi na Habila wannan karbar ita take nuna takawarsa da fifikonsa a wajan Allah a kan dan’uwansa Kabila, saboda haka ne Kabila ya yi masa hassada. Duk da gaskiya ta bayyana Allah (S.W.T) ya kunyata Kabila ya tabar da aniyarsa kuma ta bayyana a fili cewa ma’abocin daraja shi ne Habila (A.S) amma mugun ciwon nan na hassada da aka saba yi wa bayin Allah ita bai hana shi ya fasa mummunar aniyarsa ta kashe dan’uwansa ba. Saboda haka sai ya kashe shi ya gudu daga babansa ya ci gaba da yada barna da gaba da babansa. Haka nan bayan haihuwar HibatulLahi wasiyyin Annabi Adam (A.S) wato Annabi Shis (A.S) sai batacce Kabila ya dauki aniya sai ya ga bayansa kamar yadda Abu Lahab ya rika yi wa Manzon Allah (S.A.W), ya tara runduna da shi da zuriyarsa suka yaki Hibatullah (A.S) suka kore shi zuwa wani tsuburi daga tsuburan kogunan Duniya da shi da zuriyarsa.

Haka nan sarakuna daga zuriyar Kabila suka ci gaba da mulki har suka kai ga juyar da mutane daga Tauhidi da karkatar da su daga hanyar shiriya, suka kirkiro giya da gumaka har ta kai ana bauta wa irin su Ya’uka, da Yagus, da Nasra, da Suwa’a, da Wudda, da sauran gumaka, al’amarin da ya sanya Ubangiji (S.W.T) ya aika Annabi Nuhu (A.S) zuwa ga sarakunan lokacinsa ya zauna a cikinsu shekara dubu ba hamsin, an yi sarakuna da dama da sukan zo su wuce amma al’umma ba ta yi imani da shi ba har Allah ya halakar da ita da Dufana.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 next