ZamaninJuyin Juya Hali



5- Karan hancinsa mai siriri ne mai daukaka wanda yake da dan tudu.

6- Digo a kumatunsa na dama kamar tauraro mai walkiya.

7- Idanuwansa masu haske ne masu kaifin gani[8].

Kuma zai bayyana yana da kamanni na shekara 40 ne, al’amarin da zai yi wa wasu nauyin imani da shi.

3- Na Uku: Farawar Juyin Juya Hali

Ruwayoyin Shi'a da Sunna[9] sun zo game juyin imam Mahadi (A.S) wanda zai zo bayan cikar mukaddimominsa da shiryawar duniya don karbarsa, wanda zai fara daga Makka. Kuma za a yi bishara da shi ta hanyar sauti mai tsawa daga sama da safe kamar yadda ya zo a wasu ruwayoyi, da kuma tsawa ta biyu daga yamma bayan faduwar rana ko kuma ranar da take biyo wa bayan taron ma’abota bata da barna[10].

Game da farawar wannan juyin Imami na biyar yana cewa: “Na rantse da Allah! ina ganin sa ya bayyana yana mai jingina da Hajarul aswad yana ce: Ya ku mutane mu muna neman taimakon kowa a kan mutanen da suka zalunce mu, kuma suka kwace mana hakkinmu… Ni ne marayan Adam, a jiyar Nuh, zabin Ibrahim…[11]

A farkon bayyanar imam (A.S) zai yi hudubarsa[12] mai tarihi tsakanin rukunin hajarul aswad da makamu Ibrahim (A.S), kuma farkon wanda zai yi masa bai’a shi ne Jibril (A.S) bayan nan sai sahabbansa 313, kamar yadda ya zo daga imam Bakir (A.S)[13].

Sai dai wasu littattfai sun ambaci inda zai bayyana da cewa a wani kauye ne mai suna “Kur’a” a Yaman, wannan al’amari ya zo a littattafai kamar Albayan, da Alhawi, da Kashful gumma, da Al’malahim wal fitan[14]. Kamar yadda aka samu wasu ruwayoyi sun yi nuni da cewa daga birnin Kum ne motsinsa na juyi zai fara[15].

Sannan domin yada juyinsa sai ya fita daga Makka yayin da mutane dubu goma zasu yi masa kawanya kamar ta zobe, Jibrilu yana damansa, Mika’ilu yana hangunsa, sannan sai ya kada tutar Manzon Allah yana sanye da sulkensa, a hannunsa akwai takobin zulfikar[16].

Daga nan ne zai doshi Madina sannan sai Kufa wacce ita ce hedkwatar imam Mahadi (A.S), abin da ake nufi da Kufa ya hada har yankin Najaf.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next