ZamaninJuyin Juya Hali



Mafi yawancin ruwayoyi sun zo ne game da haihuwar wannan imami mai girma, al’amarin da yake nuna rashin yiwuwar karyar wannan ruwayoyi game da wannan hakika, ta wani bangare kuwa mun samu imaman Shi'a sun yi magana game da wannan al’amari na jagoran karshen duniya ba su taba yin shiru game da shi ba[3].

Shi'a sun yi imani da wannan jagora ma’asumi a karshen zamani wanda yake a cikin wannan duniya a raye, kuma masu sani da hakkinsa suna haduwa da shi, kuma samuwarsa ta tabbata ga mutane masu yawa ta hanyar tajriba, kuma da yawa daga mutane sun samu ganinsa da labarai masu yawa suka zo game da hakan, sun kuma rawaito labaru masu yawa game da shi (A.S).

Dadi kan haka kuma yana shiryar da wakilansa, wato malamai wadanda su ne tsaka-tsaki tsakaninsa da mutane a kan al’amura masu yawa da suka shafi fatawa da shiryarwa. Allama majlisi a littafinsa na Biharul anwar ya kawo kusan sa hannun wasikarsa a shafi 48 a babin “abin da ya zo na sa hannunsa” wanda ya hada da al’amarin fikihu da akida da sauransu[4]. Kamar yadda ya kawo shafi 118 karkashin taken “babin ambaton wanda ya gan shi (A.S)” da sauransu[5]. Bayan haka nan Allama Haji Mirza Husain Nuri ya kawo dalla-dalla na bayanin haduwa da imam Mahadi (A.S) yana mai nuni da abin da ya zo a Biharul anwar a littafin Jannatul ma’awa a shafi 117, a haduwa daban-daban har zuwa 59[6].

Hanzari ba gudu ba, muna iya cewa samuwar wannan mahanga ya sanya samuwar wasu masu da’awar karya na ganin imam Mahadi (A.S) a tsawon tarihi da muna iya ganin misalinsu kamar Sayyid Ali Muhammad bab Shirazi.

Jagoran juyi a mahangar Shi'a a karshen zamani: Ma’asumin mutum shi kadai ne jagoran dan Adam wanda yake samamme a dukkan sasannin duniya a lokaci guda wanda yake ya salladu a kan dukkan al’amuran da suke faruwa da sanin siffofinsu dalla-dalla, wanda samuwarsa ta zama dole ko a boye ko bayan bayyanarsa domin ci gaban samuwar duniya, in ba haka ba duniya zata kisfe da mutanenta ne[7].

Shi ne mai shiryar da mutanen duniya gaba daya wanda yake dauke da tutar shiriya da tsira da arzuta, da zagorancinsa ne dukkan wata tutar zata fadi kasa. A mahangar Shi'a sunansa da kinayarsa irin na Manzo ne (S.A.W), kuma shi ne cikon wasiyyai halifan Allah a bayan kasa, mai gyara kowa, ragowar na Allah, ma’abocin zamani, mai daukar fansar alayen Muhammad, mahangar Shi'a ta yi bayanin dukkan abin da ya shafe shi karara, wasu daga siffofinsa sun zo kamar haka:

1- Shi ne ya fi kowane mutum kama da Annabi ta fuskancin halitta da dabi’a.

2- Fuskarsa fara ce mai kyalli da aka cakuda da ja.

3- Yalwar goshi fari mai haske.

4- Girarsa a hade take.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next