Mace a Inuwar Musulunci



A wani lokaci ya kasance yana magana game da ita da cewa:­

"Lalle ni ina son mai son ta".13

Kuma kamar yadda ya yi magana a kan matsayinta a ranshi da yunkurin da'awarshi da tafiyar sakonshi, haka nan ya yi magana a kan `yarsa Fadimatu al-Zahara (a.s.), inda ya ce:­

"Fadimatu wata tsoka ce daga gare ni, abin da ke cutar da ita yana cutar da ni14.

Haka an taba tambayarsa cewa: Ya manzon Allah, wa ya fi soyuwa gare ka cikin iyalinka? sai ya ce:

"Fadimatu 'yar Muhammadu. 15

Daga madannan nassosi za mu fahimci matsayin mace da mutuncinta a rayuwar Annabi (s.a.w.a.) da da'awarsa, kuma wannan matsayi na Annabci yana misalta tunanin Musulunci na mafi girman daga matsayin mace na mutuntaka da girmama ta.

Watakila ta hanyar wannan takaitaccen bayani na Alkur'ani da tarihi za mu gane cewa mace a fahimtar AlKur'ani da sakon Allah, ita ce mai renon manyan Annabawa (a.s.), wadda ke dawainyar kare su da lura da su da tsayuwa a gefensu; wannan na bayyana karara a rayuwar Annabi Ibrahim, Musa, Isma'il, Isa da Muhammadu (Amincin Allah ya tabbata gare su baki daya), manyan Annabawa da Manzanni (a.s.), jagororin tunani, kawo gyara da wayarwa a doron kasa.

Hakika AlKur'ani ya zana mana gudummawar mace a rayuwar Annabi (s.a.w.a.) da kiransa, da shigar ta cikin hijira da jihadi, kafada kafada da gudummawar namiji, a lokacin da yake magana game da hijira, mubaya'a, mika wilaya, cancantar lada da babban matsayi, alakar namiji da mace da wasun su, a cikin daruruwan ayoyi na bayanai da maganganunsa a kan wadannan al'amurra, kamar fadarSa Madaukaki:­

"Muminai maza da muminai mata kuwa, masoya juna ne; suna umurni da aikata alheri kuma suna hani da daga mummunan aiki..."Surar Taubati, 9:71.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next