Mace a Inuwar Musulunci



Wannan ka-ce-na-ce na wayewa da ya faru a Jamus da yadda ya kare da nasarar masu kira zuwa ga fahimtar Musulunci, yana tabbatar mana da girman Musulunci, da shirin da d'an Adam ke da shi na fahimta da karbar Musulunci, duk kuwa yadda ya kai da isa. Wannan ka'ida da AIKur'ani ya tabbatar da ita da fad'arsa:­

"Ku tafi zuwa ga Fir'auna don kuwa hakika ya yi tsaurin kai. Sannan ku gaya masa magana mai taushi, ko watakila zai karbi gargadi ko kuma ya ji tsoron (azabar Allah)". Surar Daha, 20:43-44.

Daga nan za mu fahimci cewa Alkur'ani na horon masu kira zuwa ga Musulunci da su kare tunanin imani, kuma su yi magana ta Musulunci (hatta) ga wadanda suka fi kowa adawa da tsanantawa da kin imani, kuma kar su fada tarkon yanke kauna har su rufe kofar yin muhawara ta tunani.domin yanayi da halayen da ba a karbar zantukan Musulunci a cikinsu suna da sabani daga wata marhala zuwa wata, kuma daga wani yanayi na rai, zamantakewa, al'adu da tarihi zuwa wani; domin (da yawa daga) abin da aka ki karba a yau, ana karbarsa a gobe, kuma abin da aka ki yarda da shi ta wannan hanya, ana karbarsa ta wata hanyar.

3- Sha'awa da karkacewa ta jima'i: Watakila daga mafi bayyanar sabubban wad'annan da ke kira zuwa ga 'yancin mace ko sakewar jima'i akwai sababi na sha'awa da karkacewar jima'i. Hakika Alkur'ani mai girma ya yi magana game da wannan sababi, ya kuma bayyana had'arinsa da mummunar akibarsa. Allah yana cewa:­

"...Sai wasu suka maye gurbinsu a bayansu, wadanda suka watsar da Salla suka kuma bi sha'awace-sha'awace; to ba da dadewa ba za su gamu da gayyu (wani kwari ne na azaba a jahannama)". Surar Maryam, 19:59.

Ya kuma ce:­"An kawata son sha'awace-sha'awace na mata da `ya'ya da dukiyoyi tsibi-tsibi na zinariya da azurfa ga mutane..." Surar Ali-Imrana, 3:14.

Ya kuma ce:­ "..Wadanda kuwa suke bin sha'awace-sha'awace suna so ne su kauce mummunar kaucewa". Surar Nisa'i, 4:27.

A cikin wadannan ayoyi Alkur'ani na bayani ne game da hadarin sha'awace-sha'awace, da cewa suna samo asali ne daga jahilci da ya samo asali daga mummunan akida, da karkacewa daga madaidaiciyar hanya, wanda bayaninsu ya zo karara a wata ayar:­

"Wadanda suke kawo cikas a hanyar Allah, suna kuma son ta karkace alhali su masu kafircewa ne da ranar lahira". Surar Hudu, ll:l9.

Abin da muka gabatar na alkaluman kididdiga suna magana a kan karkacewar jima'i saboda wasu dalilai na ayyuka da Alkur'ani ya yi bayaninsu ga mutane ya kuma tsawatar a kansu.



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 next