Ziyarar Kaburbura Masu Daraja



Ziyarar Kaburbura Masu Daraja

 

Mawallafi: Ayatullahi Ja’afar Subhani

Mai Fassara: Yunus Muhammad Sani

Gyara da Tsarawa: Hafiz Muhammad Sa'id

[Al’adar Mutunce Kuma Sunnar Ubangiji]

Makabarta wani wuri ne babba a cikin birni da kauye inda yake dauke da babba da yaro mai iko da talaka daga magabata wadanda suke cikin barci mai zurfi wanda kamar ba za a farka ba.

 Ziyartar wannan wuri Wanda yake nuna gajiyawar dan Adam, sannan yana da rawar da yake takawa wajen gusar da duk nuna iko ko kwadayin abin duniya ga mutum. Mutum mai hankali yayin da ya ga wannan wuri mai ban tsoro, zai fahimci rashin tabbatuwar duniya daga kusa, sannan ya fara tunani akan mafita sakamkon fahimtar manufar halittar duniya da ya yi zai sanya ya fita daga cikin magagin dimuwa da son kai, sannan ya fara tunanin neman abin zai taimaka masa wajen rayuwar da ba ta da iyaka. Manzo (s.a.w) a kan wannan al’amari domin tarbiyyantar da al’umma yana cewa: “Ku ziyarci kaburbura domin zasu tuna muku ranar karshe”.[1] Sannan a wani wurin daban yana cewa: “Ku ziyarci makabarta domin kuwa akwai darasi gareku a cikin yin hakan”.[2]

 Sannan akwai wasu daga cikin mawakan zamani kamar Marigayi Sayyid Sadik Sarmad yayin ziyarar Kasar misra da kuma ziyarar Kaburburan fir’aunoni, sai ya yi wata a kan haka wadda take fassara hadisin Manzo (s.a.w) a kan hakan:

Ziyartar Kaburburan Masoya



1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 next