Halayen Imam Bakir (a.s)



Wasu ma'abota tarihi kamar Ibn Kutaiba sun yi kokarin ganin sun kare wannan lamari na kona hadisan manzon Allah (s.a.w) amma sun kasa. Domin idan tsoron kada a cakuda su ne da kur'ani to akwai mahardata, sannan nau'in usulubinsu ya bambanta, idan kuma tsoro kada ya zama an rubuta kuskure ne, to sai a zauna da marubutansu da sauran sahabbai domin a tabbatar da daidai ne ma'abota wadannan littattafai suka rubuta. Domin wannan shi ne abin da aka yi yayin rubuta Kur'ani, aka tabbatar da cewa kowa ya rubuta shi daidai. Hada da cewa wanda ya kona ya kira su da tatsuniyoyi ko labaru irin na Ahlul Kitabi. Dabakatul Kubura: Ibn Sa'ad; 1 / 140, Hujjiyatus Sunna: 395, Kanzul Ummal: 1/291).

Dadewar rashin nakalto hadisan manzon Allah (s.a.w) ya sanya da yawa daga al'ummar musulmi hatta da malamanta sun jahilci shari'a, don haka sai suka koma dogaro da wasu dokoki da suka kirkiro domin fitar da hukuncin shari'a.

Shugaban makarantar kiyasi Abuhanifa ya shahara da kiyasi, da ra'ayi, sai ya kasance yana fitar da hukuncin shari'a bisa ra'ayi, wannan lamarin ya sanya imamai (a.s) suka tashi tsaye wajen raddi kan wannan ra'ayi na Abuhanifa. Muna iya bayar da kiyasi mu ga misali; Idan Allah ya haramta giya, sai masu kiyasi su duba su ga cewa giya tana bugarwa, don haka sai su yi kiyasi da giya su ce; duk wani abu da yake bugarwa haramun ne, ba tare da la'akari da cewa tayiwu wannan giyar tana da wani abu da ya sanya Allah ya haramta ta.

Mafi muni kan wannan lamari shi ne idan Allah ya sanya cewa; giya najasa ce; to masu kiyasi zasu duba duk wani abu mai sanya maye sai su ba shi hukuncin najasa. Ba su sani ba ko abin da ya sanya ta zama najasa saboda wata siffa ce da take da ita da ta saba wa sanya maye, da haka ne masu kiyasi suka rusa hukunce-hukuncen shari'a masu yawa.

A nan ne zamu ga yadda aka samu shafe wasu dokokin Allah da canja su. Wannan lamarin ya sanya imam Muhammad Bakir (a.s) tashi tsaye domin ganin ya yaki wadannan lamurra da suka zo cikin musulunci, sannan sai bayansa dansa imam Ja'afar Sadik (a.s) ya ci gaba da wannan muhimmin aiki.

Imamai masu daraja sun yi nasihohi masu yawa ga masu kiyasi, sun gaya musu cewa; farkon wanda ya yi kiyasi shi ne Iblis, yayin da yake cewa; an yi Adam (a.s) da kasa, shi kuma an yi shi da wuta. A nan shedan ya yi kiyasin cewa; Wuta ma tana da cikin element kamar kasa, don haka yaya za a fifita wannan a kan waccan. (Alwasa'il, Abwabu sifatil Kadhi: Babi 6, j 18, s; 29, Usulul Kafi: Kitabu Fadhlul Ilm, j 1, s; 57.)

Bari mu bayar da misalin kiyasi domin mai karatu ya fahimci cewa; yana da hadari matuka: Idan da za a daka ta kiyasi ne, to da a gado namiji zai samu kaso daya ne mace kuwa kaso biyu domin namiji ya fi ta karfi shi zai iya yin abubuwa da ba ta iyawa. Da za a bi kiyasi a addini da ya kamata mai jinin haila ta rama salla ne ba azumi ba, domin salla ta fi girma da muhimmanci. Da za a bi kiyasi a addini da bawali ya kamata a yi wa wankan janaba ba maniyyi ba, domin najasar bawali ta fi ta maniyyi karfi, sai a yi wa bawali wanka, shi kuma mani a yi masa alwala. A nan ne zamu gane hadarin kiyasi.

Ra'ayin kiyasi bai bar fikihu ba hatta da ibadar akida sai da ya shiga, misali ra'ayi yana ganin sanya wani abu gaban mai salla don kada wani ya gindaya ya wuce ta gabansa tsakaninsa da Allah ubangijinsa, wannan lamari ne da imam Kazim yana yaro ya yi wa Abuhanifa raddinsa, ya sanar da shi cewa; Ubangijinsa ba jiki ba ne, don haka ba ya ganin wani abu zai iya shiga tsakaninsa da shi.

Banu Umayya sun yi amfani da hanyoyi hudu domin gamawa da imam Bakir (a.s), sun yi amfani da siyasa, da fikira, da rayuwa, da dukiya domin gamawa da shi:

Sai suka yi amfani da kiransa zuwa hedkwatarsu ta birnin Damishka, da yi masa kagen cewa zai kawo yamutsi da sabani tsakanin musulmi, aka kira shi har zuwa Sham amma Allah ya kare imam Muhammad Bakir daga wannan sharrin da kullin. (Imam Muhammad Bakir: Husain Asshakiri; s; 25)



back 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 next