Tarihin shi'a



 "Allah yana shafe abinda ya so kuma yana tabbarwa Asalin littafi kuma gare Shi yake." Surar Ra'ad: 39.

Abin nufi shi ne cewa Allah (S.W.T) na iya bayyana wani abu a bisa harshen Annabinsa ko waliyinSa ko kuma a zahiri wata maslaha ta sa bayyanawar sa'an nan daga baya kuma ya shafe shi ya zama ba abinda ya bayyana da farko ba, kamar yadda ya faru a kissar Annabi Isma'il (A.S.) yayin da mahaifinsa Annabi Ibrahim (A.S.) Ya ga yana yanka dan shi a mafarki.

Wato kenan ma'anar maganar Imam (A.S) sai ta zama kenan cewa: Babu wani abu da ya bayyana ga Allah (S.W.T) na daga al'amari a kan wani abu kamar yadda ya bayyana gare shi a kan Isma'ila dansa domin (Allah) ya dauke shi (Isma'ila) Kafin shi (Imam Sadik (A.S.) domin mutane su san, (cewa) shi (Isma'ila) ba Imami ba ne, bayan a zahiri ya riga ya bayyana cewa shi ne Imami bayansa saboda shi ne babban dansa.

Abu da yake da "Bada" a ma'ana kuma shi ne shafe hukunce-hukuncen shari'o'in da suka gabata da shari'ar Annabinmu Muhammadu (S.A.W) hatta ma shafe wasu daga cikin hukunce-hukuncen shi Annabin namu (S.A.W).

Hukunce-hukuncen Addini

Mun yi imani cewa Ubangiji ya sanya hukunce-hukunce wajibai da haram da sauransu daidai da maslaha da alheri ga bayinSa a cikin ayyukan, abinda maslaharsa ta zama babu makawa ya sanya shi wajibi, wanda kuma cutarwar da ke tare da shi ta kai matuka sai ya haramta shi, wanda kuwa maslaharsa ta zama da kadan ta rinjayi cutarwarsa ya sanya mana shi mustahabi.

Haka nan sauran hukunce-hukuncen, wannan kuwa yana daga adalcinsa da kuma tausasawarsa ga bayinsa kuma babu makawa ya zamanto yana da hukunci a kan kowane al'amari, babu wani abu daga cikin abubuwa da zai zamanto ba shi da hakikanin hukuncin Allah a kansa koda kuwa tafarkin saninsa a toshe yake gare mu. Kuma har ila yau muna cewa yana daga mummunan abu ya zamanto ya yi umarni da aikata abinda yake akwai cutarwa a cikinsa, ko kuma ya hana abinda akwai maslaha a cikinsa.

Wasu daga cikin bangarorin musulmi suna cewa mummunan abu shi ne kawai abinda Ubangiji ya hana, kyakkyawa kuwa shi ne abinda ya kyautata kuma ya yi umarnin aikatawa, ba wai ainihin maslaha da cutarwar a ayyukan suke ba, kuma babu kyawu ko rashin kyawu a cikin ayyukan, Wannan magana kuwa ta saba wa abinda hankali yake hukuntawa.

Kazalizaka sun halatta cewa Allah na iya aikata mummuna ya yi umarni da abu wanda akwai cutarwa a cikinsa kuma ya hana abinda yake akwai maslaha a cikinsa.ya riga ya gabata cewa wannan irin magana akwai rashin girmamawa a cikinta kwarai. Saboda wannan magana na hukunta danganta jahilci da gazawa ga Allah, (Allah ta’ala Ya daukaka, daukaka mai girma ga barin irin wadannan siffofi).

A takaice dai abinda yake sahihi a Akida shi ne, mu ce: Shi Allah T'a'ala ba Shi da wata maslaha ko fa'ida a kallafa wajibai da kuma haramta haramtattu, maslahar da fa'idojin duka suna komawa ne gare mu a dukan ayyuka, Kuma babu wata ma'ana wajen a kore maslaha ko barna game da ayyukan da aka yi umarni ko aka hana aikatawa. Allah ba ya umarni don wasa ba ya hani haka banza shi kuma mawadaci ne ga barin bukatar bayinsa.


[i]- Abinda yake bai damfara ko dogara da wuri ba.

[ii] - Abinda yake ya damfara ko ya dogara da wuri.

[iii] - karfici a nan ba irin wanda yake fitar da mutum daga Musulunci ba ne kamar yadda yake sananne cewa kafirci matakai matakai ne.

 



back 1 2 3 4 5 6