Tarihin shi'a



"Kuma Allah  ba ya son barna." Surar Bakara: 31

"Kuma ba mu halitta sammai da kasa da abinda ke tsakaninsu muna Masu wasa ba." Surar Dukhan: 205.

"Kuma ban halitta Aljannu da Mutane ba face don su bauta mini." Surar Zariyat: 56.

Wajabta Aiki.

Mun yi imani cewa Allah (S.W.T) ba ya kallafa wa bayinsa aiki sai bayan ya tabbatar musu hujja a kansu kuma ba ya kallafa musu sai abinda za su iya aikata shi kuma suke da ikon aikata shi kuma suka san shi domin yana daga zalunci kallafa aiki ga ajizi, wanda ba zai iya ba, da kuma Jahilin wanda ilimi bai isa zuwa gare shi ba, ba wai ya ki neman ilimin da ganganci ba.

Amma shi kuwa Jahili wanda ya ki neman sani da gangan alhali yana da damar samun ilimin hukunce-hukunce da ayyukan ibada to shi ne mai amsa tambaya a gurin Allah ne kuma shi za a yiwa ukuba a kan sakacinsa domin wajibi ne a kan kowane mutum ya koyi abinda yake bukata na daga hukunce-hukuncen shari'a. Kuma mun yi imani cewa: Allah (S.W.T) babu makawa Ya kallafa wa bayinsa ayyuka ya kuma sanya musu shari'o'i abinda na amfani da kuma alheri gare su a cikinta domin ya sanya su a kan hanyoyin alheri da rabauta dindindin, sa'an nan kuma ya shirye su zuwa ga abinda yake shi ne maslaha kuma ya gargade su game da abinda yake akwai fasadi da barna a cikinsa da kuma cutarwa gare su, da kuma mummunan karshe gare su, ko da kuwa ya san cewa su ba za su bi Shi ba, domin wannan tausasawa ne da kuma rahama ga bayinSa don kasancewarsu sun jahilci mafi yawancin amfanin kansu da hanyoyinsu a nan duniya da kuma lahira. Sun jahilci da yawan abubuwan da za su jawo musu cuta da hasara, Shi kuwa Ubangiji Shi ne Mai Rahama mai Jin kai a ainihin zatinSa, Shi kamala ne tsantsa wanda kuma shi ne ainihin zatinSa kuma har abada bai rabu daga gare shi.

Wannan tausasawa kuwa ba za ta gushe ba, don bayinsa sun kasance sun bijire sun ki bin sa, sun ki kayyaduwa da umarce-umarcensa kuma sun ki hanuwa da hane-hanenSa.

Kaddara

Jama'ar Mujabbira (masu ganin aikin bawa aiki ne na Ubangijinsa) sun tafi a kan cewa Allah (S.W.T) mai aikata ayyukan halittu don haka sai ya zamanto ke nan ya tilasta mutane a kan aikata sabo duk da haka kuma ya yi musu azaba, Sa'an nan kuma ya tilasta su a kan abinda ya yi umarni, duk da haka kuma ya ba su lada domin sun tafi akan cewa lalle ayyukansu tabbas ayyukanSa ne, ana dai danganta ayyukan su ne kawai a garesu domin musamaha domin su ne mahallan ayyukan na Ubangiji. Asalin wannan kuwa shi ne kasancewar su sun yi inkarin musabbabai na dabi'a a tsakanin abubuwa domin sun yi tsammani cewa hakan shi ne ma'anar kasancewar Ubangiji mahalicci, da ba Shi da abokin tarayya kuma Shi ne mai sabbabawa na ainihi ba waninSa ba. Duk wanda yake fadin irin wannan ra’ayi kuwa hakika ya danganta zalunci ga Allah Shi kuwa ya daukaka ga haka.

Wasu jama'a kuma wato Mufawwadha sun yi imanin cewa Allah ya sallama ayyuka ne ga halittu, ya janye kudurarsa da hukuncinsa da kuma kaddarawarsa daga gare su, wato danganta ayyuka gare shi yana nufin dangata nakasa gare shi, kuma samammun halittu suna da nasu musabbaban na musamman koda yake dai dukansu suna komawa ne ga musabbabi guda daya na farko wanda shi ne Allah (S.W.T).

Duk wanda yake fadin wadannan irin maganganu to lalle Ya fitar da Allah  daga mulkinSa ya kuma yi shirka da shi da halittunSa.

Kuma mun yi Imani muna masu biyayya ga abinda ya zo daga lmamanmu tsarkakakku da ke cewa al'amari ne tsakanin al'amura biyu (kuma tafarki matsakaici a tsakanin maganganun biyu) wanda irin wadannan ma'abota tsaurin kan suka gaza fahimtarsa wasu suka zurfafa wasu kuma suka yi takaita, babu wani daga cikin masana ilimi da ma'abuta falsafa da ya fahimce shi sai bayan karnoni.



back 1 2 3 4 5 6 next