Tarihin shi'a



 1- Ya kasance ya jahilci al'amarin bai san cewa mummuna ba ne.

2- Ko kuma ya kasance yana san da shi amma kuma ya aikata shi ala tilas ya gaza barin aikata shi.

3- Ko kuma ya kasance yana sane da shi ba a kuma tilasta shi ya aikata ba bai kuma gaza kin bari ba amma yana bukatar aikatawa.

4- Ko kuma ya kasance yana sane da shi, ba mai aikata shi ala tilas ba, ba kuma mai bukata ya zama ya takaita ke nan da aikata shi a bisa Sha'awa da wasa da bata lokaci.

Dukan wadannan sun koru ga Allah domin suna tabbatar da nakasa gare shi alhali Shi kuwa zallan kamala ne saboda haka wajibi ne mu hukunta cewa shi tsarkakakke ne daga zalunci da kuma aikata abinda yake mummuna.

Sai dai kuma wani bangare daga cikin musulmi sun halatta wa Allah (S.W.T) aikata mummuna (Sunayensa sun Tsarkaka) suka halatta cewa zai iya azabtar da masu biyayya, ya kuma shigar da masu sabo aljanna kai hatta kafirai ma kuma suka halatta cewa yana iya kallafa wa bayinsa abinda ya fi karfinsu da abinda ba za su iya aikatawa ba  amma kuma duk da haka ya azabtar da su idan har suka bari ba su aikata shi ba. Har ila yau kuma sun halatta zalunci na iya faruwa daga gare Shi da tabewa, da karya da yaudara, kuma ya aikata aiki ba tare da wata hikima ba, ba da manufa ba, ba da amfani ba, ba da fa'ida ba, da hujjar cewa;

"Ba a tambayar sa a kan abinda yake aikatawa su kuwa ana tambayar su." Surar Anbiya: 23.

Da yawa daga cikin irin wadannan da suka suranta Shi a kan wannan Akida tasu batacciya da cewa Shi, Azzalumi ne, mai Ja'irci, mai wauta ne, mai wasa ne, mai karya ne, mai yaudara ne, yana aikata mummuna, yana kuma barin kyakkyawa,(Allah  ya daukaka ga aikata wadannan abubuwa, daukaka mai girma,) wannan shi ne kafirci tsantsansa.

Kuma Allah Ta'ala Ya ce:

"Kuma Allah ba ya nufin zalunci ga bayi." Surar Mumin ayata 23.



back 1 2 3 4 5 6 next