Tarihin shi'a



Ba abin mamaki ba ne ga wanda ba shi da masaniya game da hikimar Imamai (A.S.) dangane da al'amari tsakanin al'amura biyu ba, da kuma hanya matsakaiciya ba a maganganun biyu ya ce wannan batu ne daga cikin al'amuran da masana falsafa a Yammacin Turai na baya bayan nan suka gano alhali kuwa Imamai sun riga su tun kafin karni goma da suk wuce. Imam Sadik (A.S.) yayin da yake bayanin hanyar nan matsakaiciya yana cewa: "Babu Jabru, (Tilastawa) kuma babu sallamawa ayyuka baki daya sai dai al'amari ne tsakanin al'amuran guda biyu.

Wannan ma'ana girmanta na da yawa manufarta kuma na da zurfi, abin nuni a takaice shi ne cewa: Hakika ayyukanmu a bangare guda ayyukanmu ne alal hakika kuma mu ne musabbabansu na dabi'a kuma suna karkashin ikonmu da iyawarmu, a daya bangaren kuma su ayyukan kudurar Allah ne kuma suna cikin karkashin ikonsa domin Shi ne mai ba da samuwa mai samar da ita, bai tilasta mu a kan ayyuka ba ballantana ya zama ya zalunce mu a kan yi mana ukuba idan har muka saba, Saboda muna da iko da kuma zabi a kan abinda muke aikatawa. Kuma bai sallama mana samar da ayyukanmu ba ballantana ya zamanto ya fitar da su daga karkashin ikonsa ba, Shi dai Shi ne Mai halittawa Shi ne kuma mai hukuntawa, Shi ne kuma mai umarni, Shi kuma Mai iko ne a kan kome, kuma a kewaye yake da bayinsa.

Ko ta halin kaka dai abinda muka yi imani da shi game da hukuncin Allah da kuma kaddara shi ne cewa sirri ne daga asirran Allah (S.W.T) duk wanda ya iya ya fahince shi yadda ya dace ba tare da kwauro ko zurfafawa ba to shi kenan, idan kuwa ba haka ba to ba wajibi ba ne Ya kallafa kansa cewa sai ya fahimce shi daidai wa daidai, domin kada ya je ya bata Akidarsa, kuma ta baci saboda wannan yana daga cikin al'amura masu wahala, har ma sun fi binciken al'amuran falsafa zurfi da babu mai iya gane su sai 'yan kalilan daga cikin mutane wannan shi abinda ya sa da yawa daga cikin ma'abuta ilimin akida suka tabe.

Don haka kallafa shi ma ga bayi kallafa abu ne da ya fi karfin mutum wanda yake daidai da sauran mutane. ya wadatar mutum ya yi Imani da shi a dunkule kawai yana mai biyayya ga maganar Imamai tsarkaka amincin Allah ya tabbata gare su cewa shi wani al'amari ne tsakanin al'amura guda biyu, babu tilastawa babu kuma sallamawa a cikinsa. Kuma shi baya daga cikin jigo daga jiga-jigan Addini ballantana ya zama kudurcewa da shi wajibi ko ta halin kaka filla-filla daram.

Bada

"Bada" ga mutum: Shi ne wani sabon ra'ayi ya bayyana gare shi wanda a da can bai kasance yana da wannan ra'ayin ba, wato ya canja himmarsa da ya yi a kan wani aiki da ya kasance yana nufin aikata shi, wannan kuma saboda Jahilci ne game da amfani da kuma nadama a kan abinda ya riga ya gabata daga gare shi.

"Bada" da wannan ma'anar ya koru ga Allah (S.W.T) domin kuwa yana daga jahilci ne da nakasa wannan kuwa ya koru ga Ubangiji Shi'a Imamiyya kuma ba su yarda da shi ba.

Imam Sadik Alaihis Salam Ya ce:

"Wanda Ya yi da'awar cewa Canji cikin wani abu ya auku ga Allah (S.W.T) game da wani abu canji irin na nadama to agurinmu wannan Kafiri ne a game da Allah mai girma. Har ila yau kuma Ya ce: "Wanda ya raya cewa wani abu na Canjin ra’ayi ya faru ga Allah wanda da ya kasance bai san shi ba jiya to ni ba ni ba shi''.

Sai dai kuma akwai wasu Hadisai da aka ruwaito daga Imamanmu wadanda suke kamar nuni da ma'anar "Bada" yadda ta gabata kamar yadda ya zo daga Imam Sadik (A.S) cewa: "Bada bai taba yiwuwa ga Allah ba kamar yadda ya yiwu gare shi ba a kan Isma'ila dana.

Don haka ne wadansu marubuta daga cikin bangarorin musulmi suka dangata Bada ga Shi'a Imamiyya don yin suka ga mazhaba da tafarkin Ahlul Bait (AS) suka sanya shi ya zama abin kyama ga Shi'a. Sahihin al'amari a nan shi ne mu fadi kamar yadda Ya fada a Alkur'ani:



back 1 2 3 4 5 6 next