Tattaunawa Ta Hudu



Amma zabin imamai kan lokacin mutuwarsu kamar yadda ka yi nuni da shi a cikin (Al- Kulaini. AL- KAAFI, p.258): Wannan ma ya yi kama da wanda ya gabata ne. kuma saboda suna sane da dukkan sababan rayuwa da mutuwa, kuma su ne suke son mutuwar saboda addini ya wanzu.

Amma ilimin imamai a kan komai kamar yadda ka yi nuni da shi a (Al- Kulaini. AL- KAAFI, p.260) da (Al- Kulaini. AL- KAAFI, p.260) Wannan ma ya yi kama da wanda ya gabata ne.

Amma batun cewa Imam Ali (a.s) ne ya hada Kur'ani mai daraja kamar yadda ka kawo ishara da (Al- Kulaini, AL- KAAFI, p.227): Wannan haka ne, amma ba yana nufin ya saba da wannan Kur’anin ba ne, ka sani hada Kur’ani yana kan ijtihadi ne na sahabbai, sai kowace aya da sura aka tsara ta bisa yadda sahabbai bisa jagorancin Zaid yake. Amma Imam Ali (a.s) ya tsara shi ne bisa yadda ya sauka ta yadda farkonsa yana da ayar Ikra’a, karshensa yana da ayar kamalar sako ne. kuma ya zo da shi ba a karbi nasa ba.

An ki karba ne ba don matanin kur’nin ba, sai dai domin a kasan kowace aya ya rubuta sababin saukarta, da sha’anin nuzul, da muhkam da mutashabih, da nasih da mansukh, da mujmal da mubayyan, da amm da khas, da mutlak da mukayyad, da tazil da tawil da sauransu na kowace aya. Al’amarin da bai yi wa wasu dadi ba aka ki karba, sai aka sanya abin la’akari shi ne abin da kwamitin Zaid ya gabatar. Don haka wannan ne Shi'a suke nufi ka koma littattafansu.

Ka sani wasu mus’hafai na wasu sahabbai sun zo da wasu tafsirai hade da su tare da matanin Kur’ani a tarihinsa, amma don me wani bai yi musu da’awar zuwa da sabon Kur’ani ba!! Ko kuwa su Ahlul Bait (a.s) ne kawai komai nasu ba za a karba ba, amma na saura daidai ne!?

Kamar yadda maganar da ka kawo a (Fasl-ul-khitaab fee tahreef kitaab rab-ul- arbab, page #4, Noori Tibri): Wannan ma ya yi kama da wanda ya gabata ne. kuma ka sani imamai (a.s) sun yi umarni da a koma wa wannan Kur’ani domin sanin ingancin abin da ake cewa; sun ce. Da ba su yarda da wannan Kur’ani ba to da sun rusa maganganunsu ke nan.

Amma abin da ka yi nuni da shi a shafi kamar haka: (Ihtijaj-e-tibri, page #382); Ban sami wannan ibara ba a wannan shafi ko na kusa da shi, sai dai abin da yake komawa zuwa ga abin da ya gabata.

Amma game da Imam Mahadi (a.s) cewa zai zo da Kur'ani na hakika da ka yi nuni da (Ahsan-ul-makaal, page #336, safdar Husain najfi): Shi ne Kur’anin da Imam Ali (a.s) ya hada kamar yadda tarihi ya kawo, kuma shi ne Shi'a suka yi imanin zuwan Imam Mahadi (a.s) da shi, saboda sharhinsa da ya gabata. Kuma ba shi da bambanci da wannan Kur’ani sai a jerin surori da ayoyi kamar yadda suka sauka suna bin juna. Kuma dukkan musulmi sun tafi a kan cewa a hada Kur’ani an samu ijtihadi ne wajen tsara inda za a sanya kowace sura ko ayoyi, wanda ya faru a marhaloli uku:

Lokacin Manzo (s.a.w): An yi yakini gaba daya ya gama sauka a wannan lokacin, amma an samu sabani kan wanda ya hada shi kamar yadda yake, a yau shin tun lokacin Annabi (s.a.w) ne ko kuwa.

Halifan farko: an hada shi an tsara shi bisa jagorancin kwamitin Zaid.



back 1 2 3 4 next